HAƊAƊƊIYAR ƙungiyar masu shirya finafinan Hausa ta Nijeriya (MOPPAN) ta yi alƙawarin samar wa da Rahama A. Ibrahim, wato matashiyar jarumar nan da ta musulunta saboda kallon finafinan Hausa, da kyakkyawan yanayi a Kano, musamman abubuwan more rayuwa.
Sakataren ƙungiyar na ƙasa, Alhaji Salisu Muhammad (Officer), shi ne ya bayyana haka a yayin wani zaman musamman da ƙungiyar ta yi da sabuwar jarumar a Kano a yau Juma’a.
Idan masu karatu za su tuna, ɗazu mujallar Fim ta sanar da ku cewa MOPPAN ta ƙudurci gano jarumar don ta karrama ta saboda wannan ƙwazo da ta yi na karɓar Musulunci da kuma bayyana matsayin ta ba tare da wani ɓoye-ɓoye ba.
To, ashe MOPPAN ta naɗa wani kwamiti na mutum biyu domin binciko inda wannan matashiya ta ke tare da tattaunawa da ita kan wasu abubuwa da su ka shafi rayuwar ta da sauran batutuwa muhimmai.
‘Yan kwamitin, Malam Ahmad S. Alkanawy da Salisu Officer, sun kira jarumar sun yi zama da ita inda su ka ji ta bakin ta kan tarihin ta da batun karatun ta, wurin kwanan ta, ƙawayen ta, tarihin rayuwar ta, tushen ta, sauran su.

Haka kuma wakilan na MOPPAN sun tattauna da ita dangane da ƙalubalen da ta ke fuskanta tun da ta karɓi Musulunci, da halin da ta ke ciki a yanzu a Kano, da inda ta ke zaune, a hannun wa ta ke, da ma batun ilimin addinin tun bayan karɓar kalmar shahada.
A wani rahoto da Officer ya kai wa jagororin MOPPAN a guruf ɗin su da ke WhatsApp kan zaman da su ka yi da Rahama, ya sanar da su cewa, “A kuma matsayin mu mun yi ƙoƙarin nusar da ita ‘reality’ na rayuwar Musulunci, mun nusar da ita matsayin ta a yanzu, matsayin wannan masana’anta da mu ‘ya’yan masana’antar a gare ta, sannan mun tabbatar mata da farin cikin kowa a kan wannan yunƙurin ta na neman rabauta.
“Sannan mun tabbatar mata da cewar za mu kula da lamarin ta domin fatan mu ta zama ‘role model’ a wannan masana’anta, abar kwatance, tare da taimaka mata domin samun rayuwa madaidaiciya.”
Wakilin mujallar Fim, wanda ya halarci zaman, ya ruwaito cewa an shafe kusan awa biyu ana yi wa Rahama tambayoyi, inda a ƙarshe aka tashi da ƙudirin za a faɗi lokacin da za a yi zama na gaba domin ganin an samu damar aiwatar da duk abin da ya kamata.
Mujallar Fim ta fahimci cewa a zama na biyun da za a yi da jarumar, za a gayyato yawancin shugabanni da dattawan Kannywood.
