• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Saudiyya za ta bude gidajen sinima a karo na farko cikin shekara 35

by DAGA IRO MAMMAN
April 6, 2018
in Labarai
0
Saudiyya za ta bude gidajen sinima a karo na farko cikin shekara 35
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MA’AIKATAR Al’adu da Watsa Labarai ta Saudi Arebiya ta bayyana cewa ta bada lasisi a karo na farko ga wani kamfanin Amurka mai suna AMC domin ya rika gudanar da gidajen sinima a kasar.

Ministan Al’adu da Watsa Labarai, Awwal Alawwad, ya fada cikin wata sanarwa a ranar Laraba, 4 ga Afrilu, 2018 cewa kamfanin AMC zai bude gidan sinima na farko a Saudiyya a Riyadh, wato babban birnin kasar, a ranar 18 ga Afrilu.

Ya kara da cewa, “Bada wannan lasisi na farko wata dama ce ta bude hanyoyin samar da kasuwa ga masu shirya finafinai.”

Alawwad ya kara da cewa kasuwar finafinai a Saudiyya babba ce domin kuwa yawancin al’ummar kasar matasa ne ’yan kasa da shekara 30 wadanda kuma su ka zaku su rika kallon finafinan su a gida.

Tun a watan Disamba ne hukumomin Saudiyya su ka bada sanarwar cewa za su sake soke dokar da su ka sa kan gidajen sinima shekaru 35 da su ka gabata.

A cewar ministan, Saudiyya na sa ran cewar za a gina kimanin sinimu guda 350 masu dauke da dakunan kallo guda 2,500 kafin shekara ta 2030.

Wannan mataki ya na daga cikin tsare-tsaren kasar na shirin Mahangar Shekarar 2030 wanda Yarima Mai Jiran Gado Muhammad bin Salman ya kaddamar da nufin sama wa ’yan kasuwa damar yin huldodi a kasar tare da habaka tattalin arzikin kasar.

Shi dai Yarima Muhammad bin Salman, dan shekara 32, shi ne ake kyautata zaton ya sa aka cire dokar nan da ta hana mata tuka mota da kan su a kasar, wanda zai fara aiki daga watan Yuni mai zuwa.

Kwanan nan kuma ya bayyana cewa saka hijabi bai zama tilas ba in dai za su rika yin shigar da su ke ganin ta kare mutuncin kan su.

Rufe gidajen sinima da aka yi, da hana mata tuki, da kuma tilasta saka hijabi a shekarun baya duk dokoki ne da aka kafa a bisa fatawoyin wasu malaman kasar.

Masu lura da al’amuran yau da kullum sun ce soke wadannan dokoki wani mataki ne da Saudiyya ke dauka don sauya kallon da ake mata na kasa mai tsattsauran ra’ayin addini.

Loading

Previous Post

Kotu ta ba jarumin finafinan Indiya Salman Khan daurin shekara 5

Next Post

Babban ɗan Adam A. Zango ya zama mawaƙin hip hop

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Ali Haidar Zango, mai laƙabin "Star Boy"

Babban ɗan Adam A. Zango ya zama mawaƙin hip hop

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!