
SHAHARARREN mawaƙi Alhaji Dauda Adamu Abdullahi (Rarara) ya yi rabon kayan abinci da kuɗi ga mutanen ƙauyen su na Kahutu da ke Ƙaramar Hukumar Ɗanja a Jihar Katsina.
Mawaƙin ya yi rabon kuɗi kimanin miliyan hamsin (N50,000,000) da kayan abinci ga sama da mutum 10,000 a wani gagarumin gangamin jama’a da aka yi a garin a shekaranjiya Asabar, 17 ga Agusta, 2024.
Rarara ya ba kowane mutum ɗaya kayan abinci da kuɗin cefane N5,000.
A wannan karon, mahaifiyar mawaƙin, Hajiya Halima Adamu, ta halarci filin da aka yi taron tare da jikokin ta, inda ta yi amfani da wannan damar ta yi wa jama’a godiya game da irin addu’o’i da gudunmawar da suka ba ta a lokacin da ‘yan bindiga su ka yi garkuwa ita kwanan baya.

Lokacin da ya ke jawabi a wurin rabon, Rarara ya yi kira ga dukkan waɗanda su ka halarci taron da cewa, “Duk wanda ya zo wurin nan zai samu, har da waɗanda ba a gayyata ba. Don haka kowa ya ba da haɗin kai don a yi abin a kan lokaci.”
Haka kuma ya ce al’umma su ƙara haƙuri, nan da wata shida talauci zai zama tarihi a ƙasar in-sha Allahu.
Sannan ya ƙara da cewa, “Duk wanda ka gani a wurin rabon nan, shi ma ba haka ya so ba, domin shi ma ya na so a ce ya bayar ga mabuƙata.”

Mujallar Fim ta ruwaito cewa a cikin wannan shekarar, Rarara ya yi irin wannan rabon aƙalla sau biyar daga watan azumi zuwa yanzu.
Da yawa mutane su na ganin irin wannan taimakon da mawaƙin ya ke yi wa al’umma ya na ɗaya daga cikin abin da ya sa har yanzu ya ke jan zaren sa a harkokin sa ta kowane ɓangare.
Rarara dai ya yi suna wurin taimakon al’umma, ba mutanen ƙauyen su kawai ba, har ma a cikin masana’antar Kannywood da kuma sauran jama’a na wasu jihohin.

Duk da cewa ana cikin wani hali na matsin rayuwa a ƙasar nan, amma mawaƙin bai gaza ba wurin taimako.
A cikin ‘yan siyasar da ya ke hulɗa da su da kuma manyan masu arzikin ƙasar nan, ana iya cewa babu wanda ke kwatanta abin da mawaƙin ke yi.
