INNA lillahi wa inna ilaihir raji’un! Allah ya karɓi ran shahararren ɗan wasan kwaikwayo kuma tsohon ma’aikacin Rediyon Nijeriya Kaduna, Alhaji Usman Baba Pategi, wanda aka fi sani da Samanja Mazan Fama.
Samanja ya rasu a daren jiya Asabar, 11 ga Nuwamba, 2023 a wani asibitin kuɗi mai suna Garden City da ke Titin Sultan cikin garin Kaduna, bayan doguwar jinya da ya yi fama ita.
Marigayin, mai kimanin shekaru 81 a duniya, ya rasu ya bar mata biyu da ‘ya’ya 14.

Za a yi jana’izar sa a yau Lahadi, 12 ga Nuwamba, da misalin ƙarfe 10:00 na safe, a masallacin Juma’a da ke Ja’afaru Estate, Kabala Costain, Kaduna.
Allah ya jiƙan shi da rahama, ya albarkaci dukkan abin da ya bari, amin.