WATA sabuwar jarumar Kannywood mai suna Rahama A. Ibrahim ta bayyana cewa kallon finafinan Hausa ne ya ba ta sha’awar shiga Musulunta tare da shigowa masana’antar finafinan Hausa don ta bada gudunmawar ta ta hanyar fim.
Matashiyar, ‘yar asalin garin Kumo da ke Jihar Gombe, ta bayyana haka ne a wata hirar bidiyo da aka yi da ita a tashar YouTube mai suna Matashiya.
A guntun bidiyon mai tsawon miti 2:05, wanda mujallar Fim ta wallafa a shafukan ta na Instagram da Facebook, Rahama ta ce kafin ta musulunta ɗin sunan ta Judith A. Ibrahim, kuma ita Kirista ce.
Rahama ta ce yadda masu shirya finafinan Hausa ke nuna yadda tsarin Musulunci ya ke tare da sanya wasu daga cikin ayoyin Alƙur’ani a finafinan shi ne abin da ya ja hankalin ta har ta kai ga ta sauya sheƙa zuwa Musulunci.
Jarumar ta bayyana hanyar da ta bi wajen ganin ta samu rabauta da Musulunci, ta ce, “Na taso a gidan mu wanda mu ke bin addinin Kiristanci. Ba mu taso mu na ba wa irin finafinan Hausa muhimmanci ba, amma duk da haka saboda ina yawan kallon finafinan Hausa, a ciki kuma da yake akwai irin ana ɗauko ayoyi a cikin Ƙur’ani, da yake da man gidan mu malamai ne na addinin Kiristanci, to akwai Ƙur’anin na Hausa da na Turanci, kasancewar babu Ƙur’ani na Larabci domin ba mu jin sa.
“Kasancewar a duk lokacin da aka faɗi wata aya a cikin Ƙur’ani, to kasancewar ina da shi, sai na buɗe na gani, sai na kwatanta shi da abin da ya ke cikin Baibul.
“A haka ne har ya sa na wa’azantu, abin ya gamsar da ni.

“Na je na samu wani malami a unguwar mu, na yi masa bayanin ga abin da na ke so na shiga Musulunci, wanda da farko ma bai yarda ba.”
Rahama ta bayyana cewa ta haɗu da ƙalubale bayan shigar ta Musulunci wanda sai da ta kai har ta yi niyyar fita daga Musuluncin. Ta ce lokacin da mahaifiyar ta ta samu labarin cewa ta shiga Musulunci, sai da hankalin ta ya tashi matuƙa, har ta na cewa za ta kashe kan ta idan ɗiyar tata ba ta fita daga sabon addinin nata ba.
Ta ce, “Har na koma wurin malamin da ya musuluntar da ni na ce masa, ‘Malam, zan fita daga cikin addinin Musulunci. Me ake faɗa a fita?’ Sai irin ya yi min tsawatarwa, ya kuma ce min, ‘Wannan shi ne iya abin da za ki iya samu a nan duniya; wannan ƙalubalen shi ne ribar ki.’ Ya ce, ‘Ko da a ce manomi ne, za ki samu ya yi shuka ya yi shuka ruwa bai zo ba, amma kuma ya koma gobe. Shi ne ƙalubalen rayuwa.
“Idan har Allah bai jarabce ki da wannan abin ba, ta ya za a yi ki gane addinin ya na da muhimmanci kuma ya na da ƙarfi?’
“Kuma a lokacin da na shiga cikin Musuluncin ba wai an tara jama’a ba ne. Na ce masa, ‘Ni ban son a tara jama’a saboda abu ne zan yi shi tsakani da Allah’.”
Finafinan da su ka ja hankalin ta har ta kai ga ta shiga Musulunci dai sun haɗa da ‘Ana Muslim’, ‘Ahlil Kitab’, ‘Ga Duhu Ga Haske’ da kuma ‘Asahabul Kahfi’.
Ganin bidiyon inda Rahama ta yi waɗannan bayanai ya faranta ran ‘yan Kannywood da sauran jama’a da dama, ta yadda duk wanda ya kalla sai ya ce, “Masha Allah,” kuma ya yi wa jarumar addu’ar fatan alheri.
Mujallar Fim ta samu labarin cewa uwar ƙungiyar ‘yan Kannywood, wato MOPPAN, ta shirya kiran jarumar domin ta karrama ta saboda wannan ƙwazo da ta nuna na shiga Musulunci tare da yin bayanin dalilin ta na shiga da yadda aka yi ta shiga ɗin ba tare da ta ɓoye gaskiyar al’amarin ba.