JARUMAR Kannywood, Sapna Aliyu Maru, ta bayyana cewa auren da ƙawar ta Maryam A.B. Yola ta yi jiya, na cin amana ne, domin kuwa saurayin ta ne ta aure.
Sapna ta faɗa wa da mujallar Fim haka ne bayan an ɗaura auren Maryam ɗin da wani matashi mai suna Muhammad Murtala.
A jiya Juma’a, 30 ga Satumba, 2022 aka ɗaura auren tare da Muhammad, wanda ɗan kasuwa ne kuma ɗan jarida wanda ɗan asalin Jihar Borno ne da ya ke gudanar da kasuwancin sa a tsakanin Legas da Fatakwal.

Amaryar, wadda ita ma sananniyar jaruma ce a Kannywood, ta wallafa bidiyo biyu a Instagram, ita kaɗai ta na rawar murna cikin shigar amarci a ɗaya, a ɗayan kuma ita da angon ta su na yi wa juna kallon ƙuda.
Abokan arziki da dama sun taya murnar wannan abin farin ciki da ya same ta.
Amma dai ita Sapna ta ce lallai Maryam ta ci amanar ta, domin ita da Muhammad sun daɗe da shirya maganar yin aure.
Ta yi mamakin yadda duk da kusancin ta da Maryam amma ta ci amanar ta, ta aure mata masoyi.
Sai dai ba ta yi cikakken bayani ba kan wannan iƙirarin da ta yi.
Maryam ta taɓa auren jarumi kuma mawaƙi Adam A. Zango.
Wata majiya ta shaida wa mujallar Fim cewa bayan Zango ya sake ta, ta yi wani auren wanda bai daɗe ba su ka rabu.

Daga baya ta haɗu da wani mutum, su ka ci gaba da soyayya har da alƙawarin za su yi aure. “Wannan ta sa ya ba su aron gida su ka zauna a Abuja ita da mahaifiyar ta, amma kafin a kai ga shirya maganar, sai kawai aka ji ta yi wannan sabon auren, ba zato ba tsammani.”
Majiyar ta faɗa wa wakilin mu cewa Maryam za ta tare ne a Maiduguri, Jihar Borno, inda can ne angon nata ya aje uwargidan sa da ‘ya’yan sa.

Comments 3