
ABBA Sadau, yayan fitacciyar jaruma Rahama Sadau, ya bayyana alhini kan rasuwar mahaifin su, Alhaji Ibrahim Sadau, wanda ya kwanta dama a yau. Haka kuma ya faɗa wa mujallar Fim yadda ya rasu.
Mahaifin nasu dai ya rasu ne da asuba a yau, kwana ɗaya bayan dawowar sa daga aikin Hajji. (A jiya ya dawo, ba shekaranjiya ba kamar yadda rahoton mujallar Fim na farko ya ambata).
Ya rasu a asibitin sojoji mai suna 44 Nigerian Army Reference Hospital, Kaduna (Asibitin 44), da misalin ƙarfe 4:00 na asuba, bayan da ciwon sugar shi ya tashi.
An yi masa sallah da misalin ƙarfe 10:00 na safe, a harabar wata makarantar Islamiyya da ke kusa da gidan sa a kan Titin Lome, Unguwar Rimi, Kaduna.
Daga nan kuma aka kai shi gidan sa na gaskiya da ke babbar maƙabartar unguwar.


Dattijon, mai kimanin shekara 58, ya rasu ya bar mata biyu da ‘ya’ya tara. Rahama ita ce ‘yar sa ta biyu.
Mujallar Fim ta yi ƙoƙarin jin ta bakin Rahama Sadau, amma haka ya faskara, saboda irin yadda jama’a suka cika ɗakin da take.
Sai dai yayan ta, Haruna Sadau Ibrahim (wanda aka fi sani da sunan Abba Sadau), ya shaida wa mujallar Fim irin halin kiɗimewar da ya shiga sakamakon wancan rashin na mahaifin su.
Abba, wanda furodusa ne a Kannywood, ya ce, “Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un! Wannan rashi ba mu taɓa yin shi ba a family ɗin mu gaba ɗaya, sai wannan karon ne muka fara samun irin wannan rashi babba, gaskiya.
“Kuma ya taɓa mu, ya taɓa kowa ma, don ni har yanzu ni ban gama yarda ba, domin jiya ya dawo daga Saudiyya, bayan ya dawo ya ce ba shi da lafiya, ya kira ni a waya ta ya ce in turo masa likita, na ce masa kamata ya yi ya je asibiti a yi masa general check-up, da yake ba yi tafiya.
“Ana kai shi asibitin, sai labari ya canza, jikin sai ya tashi sosai. Da ma yana da ciwo suga da sauran su.
“Muna ta waya da likitan da wadda take tare da shi, har dai aka ce lokaci ya yi. Allah ya ƙaddara a Nijeriya zai rasu.”


Abba ya ci gaba da bayyana yadda zai riƙa tunawa da mahaifin nasu, ya ce, “Akwai abubuwa da yawa da zan riƙa tuna mahaifi na da su, amma abin da zan fi tunawa da shi, wanda kuma zan yi koyi da shi, shi ne ibada, domin ba za a taɓa zuwa masallaci ka gan shi a sahu na biyu ba, ko da yaushe a sahun farko za ka gan shi. In dai ibada ne, a gaba za ka gan shi; an shaide shi da haka.
“In godiya ga ‘yan Kannywood da sauran al’ummar da suka halarci jana’iza. Wallahi har ƙwalla na yi saboda irin dandazon jama’a da na gani. Allah ya saka wa kowa da alkhairi.”
Wakilin mu, wanda ya halarci jana’izar, ya ruwaito cewa wasu daga cikin ‘yan fim da suka halarci jana’izar da ta’aziyya sun haɗa da Yasin Auwal, Umar M. Shareef, Yusuf Lazio, Sa’adu Cousin, Muhammad Showman, Musty Fashion, A.A. Rasheed Kabala, Abdul S.D., Hajiya A’isha NTA, da Maryam Aliyu (Madam Korede).


