• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, June 15, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

‘Yan fim ba su san mutuncin kan su ba, inji Umar Inuwa

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
April 5, 2020
in Labarai
0
Alhaji Umar Inuwa

Alhaji Umar Inuwa

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
AN yi kira ga masu sana’ar finafinan Hausa da su san abin da ya kamata su yi wajen kare mutuncin kan su da na sana’ar su ta yadda mutane za su riƙa kallon su da mutunci. 
 
Wannan kiran ya fito ne daga bakin tsohon shugaban ƙungiyar ƙwararru ta masu shirya finafinan Hausa ta ƙasa, wato ‘Motion Picture Practitioners Association of Nigeria’ (MOPPAN), reshen Jihar Bauchi, Alhaji Umar Inuwa, a lokacin da ya ke tattaunawa da mujallar Fim.
 
Alhaji Umar, wanda tsohon Manajan Darakta ne na Hukumar Talbijin ta Jihar Bauchi, furodusa ne wanda ya shirya finafinai da dama.
 
A hirar, ya bayyana harkar fim da cewa sana’a ce wadda Allah ya yi wa albarka, amma sai ya zama mafi yawa daga cikin masu yin ta ba su san yadda ya kamata su gudanar da ita ba, don haka ne ta ke ta samun matsalolin da aka kasa magancewa.
 
Ya yi nuni da cewar harkar fim ta karɓu sosai a ƙasar Hausa har ma da duniya, domin akwai mutane da yawa da ba sa jin Hausa amma su na kallon fim ɗin Hausa, sai dai rashin inganci da shiriritar da ke cikin harkar sun yi matuƙar mayar da sana’ar baya.
 
Alhaji Umar ya ci gaba da cewa: “Duk wata harka sai an koye ta, amma a yau rana tsaka sai ka ga mutum ya zo wai shi ma ɗan fim ne; sai mace ta zo kawai ita ma ‘yar fim ce, a saka ta; idan mutum ya na da kuɗi sai kawai ya zo ya yi fim.
 
“Kowa zuwa ya ke yi saboda an bar ƙofar a buɗe, babu wani tsari da aka yi na shigowa da kuma yadda ya kamata idan mutum ya shigo ya gudanar da sana’ar cikin tsari.”
 
Furodusan ya ci gaba da cewa, “Ni a matsayi na na wanda ya san harkar fim tsawon lokaci, na shigo harkar finafinan Hausa da kishin ciyar da al’umma gaba, amma a yadda na ga su na gudanar da harkar akwai matsaloli masu tarin yawa, domin na fahimce su mutane ne da duk yadda ka kai ga ilimi a kan harkar fim to sai sun nuna maka cewar kai ba ka san harkar ba.
 
“A ganin su, su kaɗai ne su ka iya, don haka duk ilimin ka sai dai ka bi su yadda su ke yi, ko da kuwa ba daidai ba ne.
 
“Sannan mutane ne da son kan su ya yi yawa, domin haka idan ka zo za ka yi harka da su, sai dai ka yi taka-tsantsan, wani lokacin ma sai dai ka kawar da kai dangane da son zuciyar su.
 
“Don haka wasu daga cikin su idan ka yi harka da su da wuya ku gama lafiya ba su ha’ince ka ba.
 
“Wannan ya sa mutane masu mutunci su ke gudun harkar, saboda halayyar ‘yan fim ɗin.
 
“A yanzu za ka ga mata su na shigowa fim, amma buƙatar su ba ta fim ba ce ko faɗakarwa, sai don biyan wata buƙata tasu ta daban kawai. 
 
“Don haka ya zama wajibi a gare su, musamman masu son cigaban harkar, da su da su tashi tsaye don ganin an inganta harkar fim tare da ciyar da harkar fim gaba, domin lokaci ya yi da harkar fim za ta tashi daga wasa ta koma sana’a kamar yadda ake yin ta a duniya.”
 
 

Loading

Previous Post

Yadda na rikiɗa daga mawaƙi zuwa jarumi a ‘Kwana Casa’in’ – Auwal Ishaq

Next Post

Dokar koronabairus: Kotu ta hukunta jaruma Funke Akindele

Related Posts

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko
Labarai

Wani maigida na ya ce wahalar banza nake yi a kan Yerima Shettima, inji Hussaini Danko

June 13, 2025
Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika
Labarai

Jarumin Kannywood, Abdul M. Shareef zai auri jaruma Maryam Malika

June 12, 2025
Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah
Labarai

Hukumar Tace Finafinai ta Kano ta yaba wa ɗakunan taruka bisa bin doka da oda lokacin bukukuwan Sallah

June 12, 2025
Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna
Labarai

Rahama Sadau ta raba barka da Sallah ga ‘yan fim na Kaduna

June 11, 2025
‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake
Labarai

‘Aure tsakanin jaruman Kannywood, Mansurah da Momoh’: Yadda lamarin yake

June 11, 2025
An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN
Labarai

An naɗa Shehu Hassan Kano shugaban riƙo na MOPPAN

June 3, 2025
Next Post
Funke Akindele sanye da ankwa, ta na murmushi a caji-ofis

Dokar koronabairus: Kotu ta hukunta jaruma Funke Akindele

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!