RUNDUNAR ‘yan sanda a Jihar Kano ta kama jarumar barkwanci ɗin nan da ta ke tashe a TikTok, wato Murja Ibrahim Kunya, a yau Lahadi.
Idan kun tuna, tun a ranar 6 ga Satumba, 2022 mujallar Fim ta ba ku labarin cewa wani lauya ya shigar da ƙorafi a wajen ‘yan sanda inda ya nemi da a binciki Murja da wasu fitattun mawaƙa masu amfani da manhajar TikTok su na “ɓata tarbiyya”.
A lokacin, Babbar Kotun Shari’ar Musulunci (Upper Shari’a Court) da ke Bichi, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Bello Musa Khalid ta aika wa kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kano takardar umarnin gudanar da bincike a kan fitaccen mawaƙi Ado Isa Gwanja da wasu mutum tara.
Umarnin, wanda aka bayar a takarda mai ɗauke da kwanan wata 30 ga Agusta, 2022, ya biyo bayan ƙarar da wasu lauyoyi su ka su ka shigar kan shi Gwanja da mawaƙi Mubarak Abdulkarim (Mr. 442), Safeeya Yusuf (Safara’u), Ɗanmaraya, Amude Booth, Kawu Ɗansarki, Murja Ibrahim Kunya, Ummi Shakira, Samha M. Inuwa da Babiyana a kan zargin ɓata tarbiyya.
A takardar, wadda mujallar Fim ta samu kwafen ta, an lissafa sunayen lauyoyin kamar haka: Badamasi Sulaiman Gandu, Muhammad Ali Hamza, Abba Mahmud, Muhammad Nasir, L.T. Dayi, G.A. Badawi, Sanusi I. Umar da A.T. Bebeji.
An kama Murjar ne yayin da ta ke tsakiyar shirye-shiryen shagalin bikin murnar zagayowar ranar haihuwar ta.
Rundunar ‘yan sandan ta Kano ta bayyana a yau cewa ta kama jarumar ne bayan ƙorafin da Zauren Malaman Kano su ka yi a kan ta da wasu masu amfani da TikTok.
Sai dai zuwa yanzu labarin da mujallar Fim ta samu ta ƙarƙashin ƙasa wanda ba mu tabbatar da shi ba ya nuna cewa tuni wasu manyan mutane su ka shiga sahun neman a saki Murja din.