GWAMNAN Jihar Filato, Mista Simon Bako Lalong, wanda shi ne Darakta-Janar na Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Shugaban Ƙasa na jam’iyyar APC, wato ‘Presidential Compaign Council’ (PCC), ya amince da naɗin wasu ‘yan Kannywood a matsayin membobin kwamitin.
‘Yan Kannywood ɗin sun haɗa da Abdul Amart Mohammed a matsayin darakta da Isma’il Na’abba Afakallah a matsayin mataimakin darakta, sai Sani Mu’azu a matsayin sakatare da su Ali Nuhu da sauran su a matsayin membobi.

A sanarwar naɗin wadda daraktan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na gwamnan, Dakta Makut Simon Macham, ya fitar a yau Talata, an bayyana cewa naɗin ya biyo bayan tabbacin da ɗan takarar Shugaban Ƙasa a APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa masana’antar ta Kannywood a lokacin da su ka gudanar da taro a Kano wanda Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya shirya, inda ya haɗu da wasu daga cikin manyan ‘yan Kannywood.
‘Yan fim ɗin sun gudanar da wasanni, kuma su ka yi alƙawarin yin aiki tuƙuru don ya cimma nasara.
Shi kuma Tinubu ya yi masu alƙawarin ba su dama a cikin kamfen ɗin sa don su goya masa baya burin sa na zama shugaban ƙasa Nijeriya ya cika, bayan sun nuna fasahar su a gaban ɗan takarar.
A taron, Gwamna Lalong ya bauƙaci ‘yan Kannywood ɗin da su tattaro masoyan su don a haɗu a mara wa Tinubu baya, tare da kira a gare su da su ba da himma wajen tallata shi da manufofin sa ga jama’ar ƙasa.

