• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Thursday, May 14, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Za mu yaƙi Arewa24 a kotu kan ɓarnar da ke cikin ‘Kwana Casa’in’ – Afakallah

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
April 8, 2020
in Labarai
0
Hukuma na ƙorafi da inda maza su ka kama hannayen mace a shirin 'Kwana Casa'in' na ranar Lahadi

Hukuma na ƙorafi da inda maza su ka kama hannayen mace a shirin 'Kwana Casa'in' na ranar Lahadi

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram
HUKUMAR Tace Finafinai ta Jihar Kano ta bayyana cewa ko da wasa ba za ta yarda tashar Arewa24 ta ci gaba da nuna shirin diramar nan na ‘Kwana Casa’in’ ba domin ya na ɗauke da abin da ta kira baɗala.
 
Haka kuma ta ce matsayin ta a kan lamarin ya yi daidai da dokar da ta kafa ta.
 
Shugaban hukumar, Alhaji Isma’il Na’abba (Afakallah), shi ne ya bayyana haka a hirar da ya yi da mujallar Fim ɗazu.
 
Ya ce zai maka Arewa24 a kotu idan har tashar ta bijire wa umarnin sa.
 
A jiya ne Afakallah ya umarci tashar talbijin ɗin da ta ɗage nuna wasannin ta biyu mafi farin jini ga ‘yan kallo, wato ‘Kwana Casa’in’ da ‘Gidan Badamasi’, domin ba a ba hukumar sa ta tace su ba kafin a watsa su a duniya.
 
A hirar sa da mujallar Fim a yau, Afakallah ya bayyana cewa idan har Arewa24 ba su bi umarnin ba, to hukumar za ta mata su a kotu.
 
Ya ce: “Lallai abin da mu ka yi ya na bisa doka, domin a yadda ake nuna shirin ya saɓa wa ƙa’idojin mu na addini da al’adun ƙasar Hausa.
 
“Don haka dole ne mu sauke nauyin da ya ke kan mu na kiyaye dokoki da ƙa’idoji, don bai kamata mu bar wannan ɓarnar ta cigaba ba.
 
“Wannan ya sa mu ka ba su lokaci da su dakatar da shirin tare da cire waɗannan wuraren masu nuna baɗala.”
 
Da wakilin mu ya tambaye shi idan hukumar tasa ta na da iko a kan gidan talbijin ɗin da ba a Kano shirye-shiryen sa su ka tsaya ba, sai ya ce, “To idan ma ba iya Kano ya tsaya ba, a ina ofishin su ya ke? Ta ina su ke yaɗa ayyukan nasu?
 
“Tun da a Kano su ke yi, ya zama dole su bi dokokin Kano, idan kuma ba haka ba sai mu je kotu, idan mun je sai a tantance.
 
“Mu dai a matsayin mu na waɗanda nauyin jama’a ya ke kan mu, mun fita haƙƙi, don haka ba za mu bari ana yaɗa ɓarna ba sai inda ƙarfin mu ya ƙare.
 
“Kuma jama’a shaida ne daga lokacin da aka fara nuna cigaban shirin, ka ji yadda ake ƙorafi saboda irin rungumar mata da ake yi. 
 
“To idan mu ka bari, nan gaba ma za a nuno wajen da ake saduwa. Don haka ne mu ka ce a tsayar da shirin domin a cire abubuwan da ba su dace ba.”
 
Tun daga jiya dai matakin hukumar ya haifar da muhawara a cikin jama’a, musamman a soshiyal midiya, inda wasu ke suka wasu kuma na yabo.
 
Akwai masu cewa hukumar ta shiga hurumin da ba nata ba, yayin da wasu ke ganin abin da ta yi ya dace.
 
Masu sukar tashar sun yi nuni da wani waje a cikin ‘Kwana Casa’in’ da aka nuna a ranar Lahadi da ta gabata inda ‘yan daba su ka kamo hannayen wata yarinya su ka kawo ta gaban ogan su da ke tsaye a waje.
 
Wurin ne Afakallah ya ce maza sun rungumi mace.
 
A tsarin finafinan Hausa, ba a bari jikin mace ya shafi na mace ko ta halin ƙaƙa.
 
Tun jiya mujallar Fim ta ke ƙoƙarin jin ta bakin ɓangarorin biyu.
 
Wakilin mu ya ji wasu daga cikin ma’aikatan Arewa24, musamman ɓangaren masu rubuta labaran dirama, su na cewa za a ci gaba da nuna shirye-shiryen kamar yadda aka saba ba tare da an kai wa hukumar ta duba ba.
 
Wani daga cikin su wanda ya ce a sakaya sunan sa domin bai da ikon yin magana da yawun gidan talbijin ɗin ya ce Arewa24 ta yi rajista ne da hukumar kula da gidajen rediyo da talbijin ta ƙasa (National Broadcasting Commission, NBC), don haka wata hukumar gwamnatin Kano ko ta wata jiha ba ta da ikon dakatar da wani shiri nata.
Wasu mutanen sun yi ƙorafi da wajen da ake fitar da Fa’iza daga babban shago

Loading

Previous Post

Koronabairus ta hana ɗaukar shirin ‘The Right Choice’

Next Post

A kai na dokokin Afakallah ke ƙarewa, inji Adam Zango

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Adam A. Zango

A kai na dokokin Afakallah ke ƙarewa, inji Adam Zango

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!