A YAU Asabar, 1 ga Oktoba, 2022 aka ɗaura auren matashin jarumi a Kannywood, Haruna Shu’aibu (Ubalen Danja) da masoyiyar sa Nana A’isha Kabir (Ummi).
An ɗaura auren da misalin ƙarfe 1:15 na rana a Masallacin ‘Yanlilo da ke Tudun Wada, Kaduna, a kan sadaki N100,000.

Kafin ranar, an yi wasan ƙwallon ƙafa a dandalin Murtala da ke Titin Race Course, Kaduna.
Ubale ya na ɗaya daga cikin manyan yaran jarumi Sani Musa Danja.
Ya na cikin fim mai dogon zango na ‘Gidan Danja’, wanda tashar Arewa 24 ke nunawa.
Allah ya ba su zaman lafiya da zuri’a ɗayyiba, amin.