• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ba ɗan siyasar da zan yi wa waƙa sai ɗan Kwankwasiyya – Tijjani Gandu

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
October 16, 2022
in Mawaƙa
0
Tijjani Gandu

Tijjani Gandu

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MAWAƘIN yabon Manzon Allah (s.a.w.) wanda kuma ya ke yagar rabon sa a waƙoƙin siyasa, Tijjani Gandu, ya bayyana cewa babu wani ɗan siyasa da zai iya yi wa waƙa sai ɗan Kwankwasiyya, musamman a Kano.

Ya faɗi haka ne a lokacin da ya ke tattaunawa da mujallar Fim.

A yayin da ya ke magana kan waƙoƙin siyasa, Malam Tijjani ya ce: “Ai kowa ya sani, babu wata waƙa da aka san ni da ita sai waƙar ‘Abba Gida-Gida Abba’, waƙar da ta yi tashe a zaɓen 2019 da ya gabata, kuma ina alfahari da ita don waƙa ce da ta ɗaga daraja ta a duniya.

“Kuma ni da man a siyasa ni mawaƙin Kwankwasiyya ne. In dai a Kano ne, babu wani ɗan siyasa da zan yi wa waƙa sai ɗan Kwankwasiyya da ‘yan cikin ta. Kamar yadda ka ji mu na cewa, ba mu fara don mu daina ba!”

Wani abu shi ne ba kowa ba ne ya san yadda Tijjani ya shiga harkar waƙa, amma ya faɗa a hirar sa da wakilin mu, ya ce shi kan shi bai yi zaton zai zama mawaƙi ba.

Ya ce: “Ban taɓa zaton zan zama mawaƙi ba. Kawai dai alaƙa ta da mawaƙa wadda a lokacin harkar sana’a ta a cikin su ta ke, to sai Allah ya sa na zama mawaƙi.

“Saboda a tasowa ta na yi ƙananan sana’o’i, daga ciki har da zane-zane, kuma wannan sai ya sa na ƙulla alaƙa da mawaƙa.”

Da ya ke bayani kan yadda ya rikiɗe ya zama mawaƙi, Tijjani ya ce: “Duk wanda ya ke so a yi masa zane a situdiyo ɗin sa, sai ya kira ni na yi masa. To sai ya zama na shahara a cikin su, mun saba, ina zuwa na shiga kowane situdiyo na zauna har na fara koyon kiɗa.”

Ya ci gaba da cewa, “Da yake ina yin waƙoƙi na Mauludi a makarantar mu, sai ya zama na iya rubutun waƙoƙin yabon Manzon Allah da kuma na faɗakarwa. To sai na fara da na yabon Manzon Allah. Ina yi har aka fara sani na a cikin mawaƙa.”

Ya yi waƙoƙi da yawa, amma an ɗan jima ba a san shi ba. A cewar sa, waƙar da ta fito da shi aka san shi ita ce ”Yar Maye’.  “Ita ce ta sa aka san ni a duniya,” inji shi.

Mawaƙin ya yi wani kira ga abokan sana’ar sa, ya ce, “Ina kira ga mawaƙa da mu riƙe mutuncin sana’ar mu, mu kare duk wani abu da zai zubar mana da mutunci.”

Da fatan sun ji.

Loading

Tags: 'Yar MayeAbba Gida-GidaKwankwasiyyamawaƙasiyasaTijjani Ganduwaƙoƙin siyasayabon Annabizaɓen 2019zane-zane
Previous Post

Ali Nuhu ya maka jaruma Hannatu Bashir a kotu bisa zargin cin zarafi

Next Post

Ambaliya: Gwamnati ta fara kai agajin tan 12,000 na abinci a Anambra, Jigawa da wasu jihohin

Related Posts

Za a gabatar da littafin waƙoƙin Salma ɗiyar marubuciya Halima K Mashi ran Asabar
Mawaƙa

Za a gabatar da littafin waƙoƙin Salma ɗiyar marubuciya Halima K Mashi ran Asabar

August 23, 2026
‘Ya’ya biyu mata na Mudassir Kasim sun yi saukar karatun Alƙur’ani
Mawaƙa

‘Ya’ya biyu mata na Mudassir Kasim sun yi saukar karatun Alƙur’ani

August 2, 2026
Sani Danja: Waƙar ‘Barau Jigijim’ ta tayar da ƙura, ya ƙaddamar da gasa a kan ta
Mawaƙa

Sani Danja: Waƙar ‘Barau Jigijim’ ta tayar da ƙura, ya ƙaddamar da gasa a kan ta

July 15, 2026
Za a yi bikin naɗa Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa a Daura ranar Asabar
Mawaƙa

Za a yi bikin naɗa Rarara Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa a Daura ranar Asabar

December 11, 2025
Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi
Mawaƙa

Hotunan Ranar Farko ta taron tunawa da Makaɗa Kassu Zurmi

April 19, 2025
Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala
Mawaƙa

Abin da ya sa nake rubuta littafin rayuwa ta – Ala

October 28, 2024
Next Post
Kayan agajin da aka tura a Anambra

Ambaliya: Gwamnati ta fara kai agajin tan 12,000 na abinci a Anambra, Jigawa da wasu jihohin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!