INNA lillahi wa inna ilaihir raji’un! Allah ya yi wa mahaifiyar fitacciyar jaruma Halima Atete rasuwa a yau.
Hajiya Maryam Yusuf ta rasu a safiyar yau Alhamis, 6 ga Fabrairu, 2020, a wani asibiti a Abuja bayan doguwar jinya da ta yi fama da ita.
Wata majiya ta faɗa wa mujallar Fim cewa za a yi jana’izar ta a babban masallacin tarayya da ke Abuja.
Allah ya sa mutuwa hutu ce a gare ta, amin.
![]()






