• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Tsohon Ministan Shari’a, Malami ya jajanta wa Adam Zango kan haɗarin mota da ya yi 

by ALI KANO
June 17, 2025
in Labarai
0
Tsohon Ministan Shari’a, Malami ya jajanta wa Adam Zango kan haɗarin mota da ya yi 

Adam A. Zango a gadon asibiti a Kano

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

TSOHON Antoni-Janar na Tarayya kuma Ministan Shari’a, Alhaji Abubakar Malami, SAN, ya miƙa saƙon jaje ga jarumi Adam A. Zango kan haɗarin mota da ya yi kwanan nan.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa Zango ya yi haɗarin ne a hanyar sa ta zuwa Kano daga Kaduna, inda har wata mace matashiya da ke cikin motar ta rasa ran ta.

Yanzu haka jarumin yana kwance yana jinya a wani asibitin kuɗi a Kano.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Mohammed Bello Doka ya fitar a yau, Malami ya ce: “Cikin matuƙar damuwa, na samu labari maras daɗi na haɗarin motar da ya ritsa da sanannen jarumin Kannywood kuma mawaƙi, Adam A. Zango, kwanan nan, wanda ya auku a hanyar Kaduna zuwa Kano.

“Lokacin da nake gudanar da aikin Hajji a ƙasar Saudi Arebiya ne aka ba ni labarin haɗarin, to da na dawo sai na ga ya dace in aiko da saƙon jaje da kuma kyakkyawar addu’a a gare ka ta samun cikakken sauƙi cikin sauri.

Alhaji Abubakar Malami, SAN

“Gudunmawar ka a fagen ayyukan fasaha a masana’antar nishaɗantarwa ta Nijeriya, musamman ma a Kannywood, abin matuƙar a gode a yi alfahari ne.

“Ina addu’ar Ubangiji Allah (SWT) ya ba ka lafiya da kuzari da kuma ƙarin kariya.

“Ina tabbatar maka da cewa a wannan mawuyacin lokacin, muna tare da kai tare da bada cikakken goyon baya a gare ka da iyalan ka. Kana cikin tunanin mu da addu’ar mu.”

Loading

Tags: AbubakarMalamiAdamZangohaɗarijaje
Previous Post

AFMAN ta taya Sarari murnar samun damar halartar taron baje-kolin finafinan Nijeriya a Toronto da fim ɗin ‘Kakanda’

Next Post

Gwamnatin Kano za ta ɗauki nauyin taron ƙasa kan haɓaka masana’antar fasaha 

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Gwamna Abba Kabir Yusuf

Gwamnatin Kano za ta ɗauki nauyin taron ƙasa kan haɓaka masana'antar fasaha 

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!