SASHEN Koyar Da Harsunan Nijeriya na Jami’ar Jihar Sokoto ya shirya gasar rubuta wani salon waƙar baka ko rubutacciya da ya kira “waƙa kwaikwaye”.
A takardar bayanin gasar wadda mujallar Fim ta samu, an bayyana ‘waƙa kwaikwaye’ da “waƙar da ta ƙunshi hira ko musanyar magana tsakanin mutane biyu ko fiye.”
An ci gaba da bayyana cewa a irin wannan waƙa mai saurare ko karatu zai iya ganin mutanen cikin zuciyar sa, “kamar ya na kallon wasan kwaikwayo.”
Masu shirya gasar sun bada misalin irin wannan waƙar kamar haka: “A waƙoƙin baka na Kassu Zurmi ko Gambo ko Shata ko Ɗanƙwairo duk akwai irin wannan tsari.
“A waƙar Shayi wadda Kassu ya yi akwai inda iyayen ‘yan mata su ke tambayar Kassu da ya ba su labari game da Shayi wanda ‘ya’yan su su ke so ya aure su.”
A cewar jami’ar, a rubutattun waƙoƙi ma a kan samu irin wannan. Misali ita ce waƙar ‘Karuwa’ wadda Mu’azu Haɗejia ya rubuta, “don akwai inda karuwa da manemin ta su ke musayar magana, ita ta yi cikin fushi, shi kuma ya na lallashin ta.”

Mashirya gasar sun kuma bayyana cewa take ko maudu’in gasar shi ne “Matsalar Taɓarɓarewar Tarbiyya da ta Rashin Tsaro a Arewacin Nijeriya.” A kan wannan ne duk mai son shiga gasar zai shirya waƙar sa.
Ƙa’idojin shiga gasar bakwai ne, kamar haka:
1. Tilas ne waƙa ta sa mai sauraro ya ji cewa mutane biyu ne ko fiye, amma kada su wuce uku, su ke yin hira.
2. A sanya waƙar a kan takarda ko cikin odiyo ko bidiyo (a kan faifan sidi idan da hannu za a kawo) sannan a aiko ga adireshin da aka bayar.
3. Tilas mawaƙi da masu rera waƙa cikin bidiyo su kasance cikin sutura ta mutunci a al’adun Hausawa.
4. Tilas ne mai rubutacciyar waƙa shi zai rera waƙar sa da kan sa, ko ya kasance ya na nan a wurin gasar tare da wani da ya sa ya rera masa saboda wata lalura.
5. Ana so marubucin waƙa ya zo wurin taron shi kaɗai ba tare da ‘yan amshin sa ko waɗanda su ka taya shi rera waƙar sa ba, saboda su na cikin odiyo ko bidiyon da ya riga ya aiko domin kuwa kwamitin gasar ba zai ɗauki nauyin su ba idan su ka zo tare.
6. Ana buƙatar kada waƙar baka ta gaza kai ɗiya 30, kuma kada ta wuce 35; rubutattar waƙa kuma kada ta kasa baitoci 40, kar kuma ta wuce 45, kowane baiti ya kasance mai ɗango 5, wato ƙwar 5.
7. Mawaƙi ya haɗo da taƙaitaccen tarihin sa a rubuce.
Bayan haka, akwai abubuwan da aka haramta wajen shiga gasar, kamar haka:
1. Kada a kama sunan wani ko na wata ƙabila ko na wata hukuma ko na jinsi ko na wani ɓangare.
2. Kada a yi batsa a cikin waƙa.
3. Kada a kushe kyawawan al’adun Hausawa ko a ɗaukaka al’adun wasu al’ummomi a kan na Hausawa.
Za a karɓi saƙonnin masu son shiga gasar a tsakanin ranar 1-14 ga Nuwamba, 2021, sannan za a bayyana sakamakon gasar a ranar 15 ga Disamba, 2021.
Za a faɗi ranar da za a yi bikin karrama zakarun gasar daga baya.
An buƙaci masu son shiga gasar da su aika da waƙar su ta wannan adireshin na imel: gwkwaikwayessu21@gmail.com ko ta hannun Dakta Aliyah Adamu Ahmad.
Haka kuma an bada lambobin waya saboda masu so su kira don samun ƙarin bayani kamar haka: 08133314217 da 08095059926.
![]()







