MAKARANTAR nan mai suna Jammaje Academy za ta shirya taron ta na shekara-shekara kwanan nan a Kano tare da ƙaddamar da sabon littafin hikaya na Turanci wanda mamallakin makarantar ya wallafa.
Makarantar, wadda ta yi fice wajen koyar da ilimin Turanci a rassan ta da ke wasu jihohin ƙasar nan, za ta yi taron na bana ne a ranar 26 ga Disamba ɗin nan a wani ɗakin taro a Jami’ar Bayero, Kano, inda za a gabatar da jawabai tare da nishaɗantar da mahalarta.
Shugaban makarantar, Malam Kabiru Musa Jammaje, ya shaida wa mujallar Fim yadda taron zai kasance.
Ya ce, “A taron na bana mun tsara abubuwa da dama fiye da yadda muka saba shiryawa a baya domin kuwa a bikin na bana akwai jawabi na musamman wanda tsohon Mataimakin Shugaban Jami’ar Bayero, wato Farfesa A. Rasheed, zai gabatar. Bayan shi kuma akwai sauran manyan baƙi da su ma za su gabatar da nasu jawabin.”
Ya ƙara da cewa, “Bayan haka kuma kamar yadda na faɗa maka akwai sabbin abubuwa. To a wannan za mu gabatar da sabon littafin da na rubuta mai suna ‘A Gentle Breeze” wanda yake ƙirƙirarren labari ne na Turanci.
“Ka san a baya an san ni da littattafai da dama na Turanci, amma duk na koyar da adabin Turanci ne. A wannan lokacin ne na rubuta ƙirƙirarren labari. Don haka ka ga wannan ya zamar da taron na daban.
“Sannan kuma akwai fim ɗin Turanci mai suna ‘Jamilar Jammaje’, wanda shi ma za a haska shi a wajen taron.
“Shi fim ɗin ya zo da wani salo na koyar ɗalibai yadda za su koyi Turanci ne, duk da yake wasu sun ɗauka fim ɗin an yi shi ne a kan Makarantar Jammaje, to amma ba haka abin yake ba. Shi fim ɗin an shirya shi ne a kan wata ɗaliba da ta shiga Makarantar Jammaje, kuma a ƙarshe ta ce ita a rinƙa kiran ta da Jamilar Jammaje.
“Amma dai fim ɗin ya ginu a kan wayar wa da ‘yan makaranta kai tunda idan ɗalibi ya zo makaranta, yana buƙatar ka zaunar da shi ka wayar masa da kai a kan yadda zai ci nasara a makaranta.

“To shi abin da fim ɗin ya ƙunsa kenan.
“Kuma baya ga haka akwai mawaƙa da za su zo su baje kolin fasahar su, kamar su Mudassir Ƙasim, Sadi Sidi Sharifai, Abubakar Sani, Ado Gwanja da dai sauran su.
“Kuma za mu gabatar da taron ne a ranar 26 ga Disambar nan da muke ciki.
“Kamar yadda aka saba, ɗaliban makarantar Jammaje Academy za su halarta daga rassan makarantar da muke da shi 35 a duk faɗin ƙasar nan, kuma ban da ma ‘yan makarantar har ma waɗanda za su zo su kalla, za su fahimci irin abubuwan da ya kamata su yi idan sun shigo makarantar.”
![]()







