Tsohuwar jaruma a Kannywood, Fauziyya Sani (Maikyau) ta bayyana dalilin ta na buɗe sabon kantin sayar da kayayyakin adon maza da mata.
Kwanan nan jarumar ta buɗe katafaren wajen sayar da kayan Ummi Plaza bayan Jifatu a Titin Zariya a cikin garin Kano.
A lokacin da take yi wa mujallar Fim ƙarin bayani game da sabon kantin nata, Fauziyya ta bayyana farin cikin ta da kuma godiya ga Allah da ya ba ta damar mallakar kantin, ta ce ta daɗe tana da wannan burin, sai yanzu Allah ya cika mata shi.
Ta ce: “Na daɗe ina faɗi-tashi na ganin na samar da wata hanya ta kasuwanci domin rufa wa kai na asiri da sauran waɗanda suke tare da ni kuma a yanzu in-sha Allah mun kama hanyar matakin nasara.

“Duk da na daɗe ina harkar kasuwanci, amma dai a yanzu ne na samu damar buɗe wajen da zan saka kayan na kasa su yadda za a zo har wajen a saya. Don haka ina godiya ga Allah da ya ba ni wannan damar.”
Da muka tambaye ta irin kayan da take sayarwa a wajen kuwa cewa ta yi, “Kayayyaki da nake sayarwa a wajen sun haɗa da atamfofi, yaduka, leshi, jakunkuna, takalma, kayan jarirai da sauran kayayyaki da dama.
“Kuma alhamdu lillah daga buɗe wajen zuwa yanzu mun ga alamar nasara, ganin yadda mutane da dama suke zuwa domin gani da kuma sayen kaya a wajen.
“Ina godiya sosai ga ‘yan’uwa da abokan arziki da a kullum suke zuwa domin gani da kuma sayen kaya a wajen.
“Kuma ina sanar da jama’a ba wai ɗaiɗai kawai muke sayarwa ba, muna bayar da sari kuma muna turawa garuruwa ga duk wanda zai sayi kayayyakin mu a duk inda yake. Don haka muna maraba da masu sayen kaya a wajen mu.”
![]()






