DA alama, zazzafan rashin jituwar nan da ya daɗe ya na ruruwa a tsakanin Ali Nuhu da Adam A. Zango yanzu ya kau, domin kuwa sun yabi juna a bainar jama’a a shafukan su na Instagram, abin da ya jawo musayar ra’ayi a tsakanin ‘yan kallo.
Idan kun tuna, a baya an samu rashin jituwa tsakanin jaruman biyu, inda mabiyan su su ka riƙa jifar juna da munanan kalamai da su ka so su tada zaune tsaye. Cikin maganganun har da batun kai juna kotu.
Sai dai yanzu ga dukkan alamu lamarin ya wuce.
Ali Nuhu, wanda ake wa laƙabi da Sarki, ya rubuta yabon Zango wanda ake wa laƙabi da Prince (Yarima). A shafin sa na Instagram, Ali ya bayyana Zango da cewa: “Yarima na. Haɗuwar aboki da kuma ɗan’uwa abu ne na musamman. Ɗaya mu ke, kuma babu buƙatar bayani a kan hakan. Ina matuƙar girmama ka bisa irin yadda mu ka kasance kuma za mu ci gaba da kasancewa tare, Yarima na.”
Shi ma Zango ba a bar shi a baya ba, inda a nasa ɓangaren ya yi rubuta cewa: “Abubuwa da yawa sun faru tsakanin ‘yan’uwan juna da su ka daɗe tare. Kuma dole ne a samu tangarɗa, amma zai wuce kuma su ci gaba da kasancewa ‘yan’uwan juna. Haka yake tsakani na da kai (Ali Nuhu). Ina godiya bisa kasancewa ɗan’uwa na kuma shugaba na.”
Wannan batu dai ya ba jama’a da dama mamaki inda aka rasa menene dalilin su na yin waɗannan batutuwa.
![]()







