FITACCEN jarumi kuma mawaƙi a Kannywood, Garzali Miko, zai angwance a ranar Juma’a mai zuwa, 20 ga Agusta, 2021.
Jarumin na ci gaba da raba katin gayyatar bikin auren a soshiyal midiya.
Kamar yadda katin ya nuna, za a ɗaura auren Garzali da masoyiyar sa mai suna Habiba Umar Ahmad Dikwa (Yarinya) a Kaduna da misalin ƙarfe 1:30 na rana a Masallacin Fajrul Islam da ke unguwar Rigasa.

Tuni abokai ke ci gaba da baje basirar su wajen rera wa jarumin kuma gwanin rawa waƙoƙin taya murna.
Bugu da ƙari, a gobe Talata za a buɗe shagalin bikin da wasannin ƙwallon ƙafa, inda ƙungiyoyi huɗu za su fafata, waɗanda su ka haɗa da ƙungiyar Ali Nuhu da ta babban furodusa Abdul Amart Maikwashewa da ƙungiyar Jambulo da kuma ta A.C.
Allah ya kai mu, amin.
