• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, July 21, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ba ruwa na da kamfen ɗin Tinubu, inji Rahama Sadau

by DAGA ABBA MUHAMMAD
October 2, 2022
in Labarai
2
0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

JARUMAR Kannywood da Nollywood, Rahama Sadau, ta nesanta kan ta da wani jerin sunaye da jaridar ‘Punch’ ta buga mai nuna cewa ta na ɗaya daga cikin mata ‘yan fim da ɗan takarar zama shugaban ƙasa a jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa a matsayin matan da za su taya shi kamfen.

Rahama ta ƙaryata labarin ne a soshiyal midiya, a wani saƙo da ta yi da Turanci inda ta ce: “This is a fat big lieeeee…. I am not aware of this… I don’t know how my name made it to this list. Not in any way associated with this.” Ma’ana: “Wannan babbar ƙarya ce. Ni ba ni da masaniyar wannan. Ban san yadda aka yi suna na ya shiga wannan jerin ba. Babu abin da ya haɗa ni da wannan abin.”

Mujallar Fim ta ruwaito cewa ba a san jarumar da shiga harkar siyasa ba, sannan da alama ba a tuntuɓe ta ba kafin a fitar da sunayen, wanda hakan ne ya sa ta yi wannan rubutu cikin ɓacin rai da mamaki.

Ban da ita Rahama, wasu mata ‘yan Kannywood da ke cikin jerin sun haɗa da Saratu Giɗaɗo (Daso), Kyauta Dillaliya, Samira Ahmad, Fati Nijar, Mansurah Isah, Teema Makamashi, Ummi Gombe, Hadiza Kabara, Fati Karishma, Samira Saje, da Hajiyan Nas.

Mansurah Isah

Sai dai kuma tsohuwar jaruma Mansurah Isah ta yi wa Rahama, ta ce mata kuskure ne da aka saka sunan Rahama a jerin.

A cewar Mansurah: “Zuwa ga Rahama, da ma ba sunan ki ba ne wanda ki ka gani. Sunan Rahama MK ne amma da yake ke kaɗai ce Rahamar da su ka sani a Kannywood, sai su ka ɗauka ke ce. Amma kada ki damu, ba ke ba ce.”

Mansurah, wadda ta yi dumu-dumu a harkar siyasar Tinubu, ta nuna cewa su ne su ka ba da sunayen da aka gani, kuma ba su ba da sunan Rahama Sadau ba saboda sun san ita ba ta harkar siyasa.

A cewar ta, ‘yan Kudu ne su ka buga sunayen, shi ya sa su ka yi kuskure, domin ba su san Rahama MK ta cikin diramar ‘Kwana Casa’in’ ba.

Rahama Sadau dai ba ta ce wa Mansurah komai ba.

Amma ita Rahama MK, sai murna ta ke yi, domin har ta kwafe sunayen ta wallafa a shafin ta tare da godiya.

Idan kun tuna, a makon jiya mun ba ku labarin yadda aka naɗa ‘yan Kannywood biyar a matsayin waɗanda za su shiga rundunar yaƙin neman zaɓen Tinubu a babban zaɓen shekara ta 2023.

Su ne: Dauda Adamu Abdullahi (Rarara), Jadda Garko, Sani Idris Kauru (Moɗa), Nuhu Abdullahi, da Shugaban Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, Isma’ila Na-Abba (Afakallahu).

Loading

Tags: Bola Ahmed TinubukamfenMansurah IsahPunchRahama MKRahama Sadausiyasayaƙin neman zaɓeZaɓen 2023
Previous Post

Zaɓen 2023: INEC ta kafa wa ‘yan jarida dokokin hana su fifita wata jam’iyya kan wata

Next Post

A harkar fim na samu kuɗin buɗe katafaren shagon sayar da tufafi – Maishadda

Related Posts

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa
Labarai

Allah ya yi wa mahaifiyar darakta Salisu Mu’azu rasuwa

July 17, 2025
Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano
Labarai

Hukumar Shari’a da Hukumar Tace Finafinai za su haɗa gwiwa don tsaftace tarbiyya a Kano

July 11, 2025
Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 
Labarai

Jarumin Kannywood, Baba Ƙarami ya yi magana kan ganin sa da aka yi kan keken guragu 

July 10, 2025
Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a
Labarai

Tsohuwar jarumar Kannywood, Halisa tana neman addu’a

July 9, 2025
Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu
Labarai

Mawaƙin Manzon Allah, Abdullahi Ɗan Gano ya rasu

July 7, 2025
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 
Labarai

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

June 29, 2025
Next Post
Abubakar Bashir Maishadda a wajen taron

A harkar fim na samu kuɗin buɗe katafaren shagon sayar da tufafi - Maishadda

Comments 2

  1. Pingback: Ba ruwana da kamfen din Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, cewar jaruma Rahama Sadau - Kyauta Blog
  2. Pingback: Ba ruwana da kamfen din Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, cewar jaruma Rahama Sadau - Dalatop News

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!