FITACCEN jarumi a shirin diramar nan ta ‘Kwana Casa’in’, Abdul Sahir, wanda aka fi sani da sunan Malam Ali, ya bayyana cewa bai damu da surutun da wasu mutane ke yi a kan auren sa da wata ‘yar siyasa ba.
Ya bayyana haka ne a hirar sa da mujallar Fim kan yamaɗiɗi da ake yi a kan auren sa da Hon. Hajiya Bilkisu Shibah, wadda tsohuwar ‘yar takarar zama Sanata ce a Jihar Kaduna.
A ranar Asabar ɗin nan, 11 ga Afrilu, 2020 hotunan Malam Ali da amaryar tasa su ka mamaye shafukan sada zumunta.

Haka kuma an ga bidiyon da jarumin ya saki inda ya tabbatar wa da duniya cewa lallai Hajiya Bilkisu matar sa ce.
Labarin ya ja hankalin mutane ne saboda ana ganin amaryar tasa ta girme shi.
Da mujallar Fim ta tuntuɓi jarumin a kan lamarin, ya tabbatar mana da cewa lallai an ɗaura auren nasu, kuma tun kafin auren nasu sun samu fahimtar juna tare da soyayya mai ƙarfi.
Ya ce don haka ba ya gani kuma ba ya jin duk wasu maganganu da mutane ke yi a bayan fage saboda shi ne zai zauna da ita, ba su ba.
Ya ƙara da cewa ya na da burin su ƙare rayuwa tare da wannan mata tasa in-sha Allah.

![]()







