Alƙalan da ke tantance labaran da aka shigar domin Gasar Rubutu ta Ranar Marubutan Hausa ta Duniya sun fitar da sakamakon mataki na farko.
A wannan matakin, an tace an tantance labarai guda 42 waɗanda suka nuna alamar hoɓɓasa, don haka za a ba su horo gaba ɗayan su maimakon 30 da aka tsara a farkon al’amari.
Kuma an miƙa sakamakon ga kwamitin ƙoli na gasar don su tsara yadda horarwar za ta kasance.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa zakarun wannan kashi na farkon za a yi masu bita ta musamman a kan Fasahar Zamani (AI) da tsaro da tattalin arziki da kuma rubutun gajerun labarai.
Bayan bitar, za a buƙaci kowannen su da ya rubuta cikakken labarin sa wanda bai gaza kalmomi 1,000 ba kuma bai wuce kalmomi 1,500 ba bayan bitar.

Za a bayyana labaran da suka yi nasara ne a wajen bikin Ranar Marubutan Hausa ta Duniya 2025 wanda za a gudanar a ranar 31 ga Disamba, 2025 zuwa 1 ga Janairu, 2026 a Dutse, babban birnin Jihar Jigawa.
![]()







