• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Sunday, April 5, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Gwamnatin Tarayya ta ba kamfanin Lenscope Media kwangilar naira miliyan 250 domin gina Gidan Shirya Finafinai na Jos da badalar Kano

* Kamfanin zai haɓaka Masallacin Juma'a na Zariya da Fadar Sarkin Katsina

by IRO MAMMAN
February 8, 2025
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya ta ba kamfanin Lenscope Media kwangilar naira miliyan 250 domin gina Gidan Shirya Finafinai na Jos da badalar Kano

Dama zuwa hagu: Shugaban Lenscope Media, Makama Sani Mu'azu, da Darakta-Janar na NCMM, Mista Olugbile Holloway, da Barrister Babatunde Adebiyi Jim kaɗan bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar (Hoto daga: Lenscope Media)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

GWAMNATIN Tarayya ta ba fitaccen kamfanin shirya finafinai ɗin nan mai suna Lenscope Media aikin gina Gidan Shirya Finafinai na Jos (wato film village) da haɓaka wasu wuraren tarihi da ke Kano, Katsina da Zariya.

Za a gina Gidan Shirya Finafinai ɗin ne a wani ɓangare na haɓaka Gidan Tarihin Gine-ginen Gargajiya na Jos, wato Museum of Traditional Nigerian Architecture (MOTNA).

A cikin aikin haɓaka wuraren tarihin, Lenscope Media za su sake gina muhimman wuraren tarihi irin su Badalar Birnin Kano, da Masallacin Juma’a na Zariya, da Fadar Sarkin Katsina, waɗanda a da ana amfani da su a finafinan da aka shirya a Nijeriya da ma ƙasashen ƙetare.

Yanzu za a lissafa waɗannan wuraren tarihin a cikin ababen da ke ƙarƙashin Gidan Shirya Finafinai na Jos domin inganta wuraren da ake gani a cikin finafinai tare da taskace wuraren tarihi na gargajiya.

Hukumar Gidajen Adana Kayan Tarihi Da Wuraren Tarihi ta Ƙasa (National Commission for Museums and Monuments, NCMM) ita ce ta ba da kwangilar.

Hukumar da kamfanin sun rattaba hannu kan yarjejeniyar aikin a ranar Alhamis a Abuja.

Shugaban Lenscope Media, fitaccen jarumi Makama Sani Mu’azu, shi ne ya rattaba hannu a madadin kamfanin sa, shi kuma Darakta-Janar na hukumar, Mista Olugbile Holloway, ya rattaba hannu a madadin Gwamnatin Tarayya, yayin da Lauya Babatunde Adebiyi ya jagoranci rattaba hannun a taron.

Yarjejeniyar dai irin ta haɗin gwiwar gwamnati da kamfani mai zaman kan sa ce, wato Public-Private Partnership (PPP), kuma za ta shafe tsawon shekara 20.

Ana sa ran aikin zai sauya fasalin Gidan Tarihin na Jos zuwa sabon Gidan Shirya Finafinai na Jos da kuma Makarantar Koyon Shirya Fim, wato Film Training School.

Hakan zai ƙara tabbatar wa da Jihar Filato da matsayin ta na cibiyar inganta harkar fim.

Alhaji Sani Mu’azu ya sha alwashin cewa kamfanin sa zai yi amfani da ɗimbin sanin makamar aiki da yake da shi wajen dawo da martabar waɗannan wuraren tarihin da kuma sauya fasalin abin da za a riƙa yi a cikin su ta fuskar ayyukan fasaha.

Ban da batun shirya fim ma, sabon Gidan Shirya Finafinai na Jos ɗin zai ƙunshi Gidan Cin Abinci na Arewa inda za a samu abincin gargajiya iri-iri na arewacin Nijeriya, da kuma kayan hawan doki daban-daban domin yin amfani da su a finafinai, wanda hakan zai jawo mashirya fim da masu yawon buɗe ido zuwa wurin.

Kuɗin farko da aka zuba a kwangilar shi ne naira miliyan ɗari biyu da hamsin (₦250m), wanda ake sa ran zai haɓaka tattalin arzikin inda za a yi aikin, zai samar da aikin yi ga dubban matasa masu basira, kuma ya ƙarfafa matsayin Jihar Filato na babban wurin da mashirya fim daga sassan Afrika suke zuwa domin shirya fim.

Ana sa ran cewa idan har Gidan Shirya Finafinai na Jos ɗin ya fara aiki, zai inganta yadda ake shirya fim, ya haɓaka al’adun gargajiya, kuma ya haɓaka harkar yawon buɗe a Nijeriya.

Kamfanin Lenscope Media ya bayyana wannan al’amari da sunan “muhimmin cigaba ga masana’antar fim ta Nijeriya”.

Loading

Tags: Barrister Babatunde Adebiyifilm villageJos Film VillagekwangilaLenscope MediaMakama Sani Mu'azuNational Commission for Museums and MonumentsOlugbile Hollowayyarjejeniya
Previous Post

Rukuni huɗu na masu kallon fim ɗin Hausa

Next Post

Tsohon ɗan jarida Sanda Adamu Tsafe ya kwanta dama

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Tsohon ɗan jarida Sanda Adamu Tsafe ya kwanta dama

Tsohon ɗan jarida Sanda Adamu Tsafe ya kwanta dama

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!