• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Monday, August 10, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Tsohon ɗan jarida Sanda Adamu Tsafe ya kwanta dama

Shekarun sa 77

by ALI KANO
February 9, 2025
in Labarai
0
Tsohon ɗan jarida Sanda Adamu Tsafe ya kwanta dama

Marigayi Alhaji Sanda Adamu Tsafe (Sarkin Yaƙin Tsafe)

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ALLAH ya yi wa tsohon ɗan jaridar nan kuma dattijon arziki, Alhaji Sanda Adamu Tsafe, rasuwa. Shekarun sa 77.

Ya rasu a daren jiya a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo (UDUTH) da ke Sakkwato bayan ya yi fama da rashin lafiya.

Marigayi Alhaji Sanda ya yi fice a aikin rediyo a lokacin da yake aiki a gidan Rediyo Talbijin Kaduna.

Daga nan ya yi aiki a Sashen Hausa na gidan rediyon BBC.

Haka kuma ya taɓa zama Janar Manaja na gidan Rediyon Rima da ke Sakkwato, muƙamin da aka tsige shi daga kai sakamakon rikicin sarauta da ya biyo bayan rasuwar Sarkin Musulmi Abubakar na 3 a cikin 1988.

Daga bisani, an naɗa shi Kwamishinan Zaɓe na Tarayya mai kula da Gundumar Birnin Tarayya (FCT).

Alhaji Sanda sananne ne wajen taimakon jama’a da kuma ayyukan addini, musamman a Jihar Zamfara.

‘Yandoton Tsafe Alhaji Habibu Aliyu ya naɗa shi Sarkin Yaƙin Tsafe.

Shi ne ciyaman na kamfanin Adahan Universal Investment Limited.

An haife shi a cikin 1948 a garin Tsafe, inda a nan ya fara yin karatun firamare kafin ya wuce Babbar Makarantar Firamare da ke Kwatarkwashi.

Ya yi karatu a Makarantar Lardi da ke Sakkwato, da Makarantar Share Fage (SBS) ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Daga bisani, ya yi karatu a Makarantar Aikin Jarida ta London, wato London School of Journalism.

Marigayi Alhaji Sanda ya rasu ya bar matan aure biyu, da ‘ya’ya 29, da kuma jikoki 36.

Allah ya rahamshe shi, amin.

Marigayi Alhaji Sanda Adamu Tsafe

Loading

Tags: rasuwaSanda Adamu TsafeZamfara
Previous Post

Gwamnatin Tarayya ta ba kamfanin Lenscope Media kwangilar naira miliyan 250 domin gina Gidan Shirya Finafinai na Jos da badalar Kano

Next Post

‘Arewa Republic’. Kun gani ba?

Related Posts

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama
Labarai

Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama

August 2, 2026
Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11
Labarai

Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11

August 1, 2026
Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano
Labarai

Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano

July 15, 2026
Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu
Labarai

Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu

July 14, 2026
A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti
Labarai

A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti

July 9, 2026
Next Post
‘Arewa Republic’. Kun gani ba?

'Arewa Republic'. Kun gani ba?

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!