GWAMNATIN Tarayya ta ce daga yanzu ba za ta bari wani fim mai mutunta mugaye ya fito ba.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa mugaye a cikin wasan fim dai su ne mutane da ke aikata ta’asa kamar sata, fashi, fyaɗe, kashe-kashen rayuka, ta’addanci da sauran su. Da Turanci ana kiran su ‘villains’.
Hukumar Tace Finafinai da Bidiyo ta Ƙasa (NFVCB) ta ce daga yanzu ta haramta duk wani fim mai nuna cewa irin waɗannan ɓatagarin sun yi galaba ko kuma abin koyi ne.
Shugaban hukumar, Alhaji Adedayo Thomas, shi ne ya bayyana haka a cikin jawabin da ya yi a jiya Litinin, 6 ga Satumba, 2021 a wajen buɗe wani taro na kwana biyar na ƙara wa juna sani a kan tsarin tace finafinai da karkasu su don masu kallo wanda aka shirya wa wasu zaɓaɓɓun ɗaliban Jami’ar Kalaba.
A jawabin, wanda mujallar Fim ta samu kwafen sa, Thomas ya ce: “Ya dace finafinan Nijeriya su nuna gaskiyar abin da ke faruwa, to amma a ƙarshe su koyar da darussan tarbiyya. Ya kamata finafinan mu su ɗauki wata matsala, su yi aiki a kan ta amma fa a ƙarshe su nuna abin da ya faru ga masu aikata mugun abu a cikin fim.
“Amma idan ka shirya fim inda a ciki ka kambama ko ka nuna jin daɗi kan abin da wani wanda ya aikata ta’asa a kan al’adu ko zamantakewar ɗan’adam ba tare da hukunci a kan sa ba, ba za mu amince da irin waɗannan finafinan ba.”
A lokacin taron, Thomas ya bayyana cewa kamar yadda gwamnatin Buhari ke ƙoƙarin sanya ido kan muggan kalamai da ake yaɗawa a soshiyal midiya, ita ma tasa hukumar ta na duba abin da finafinan da ake turawa a Google da YouTube su ka ƙunsa. Ya ce haka kuma hukumar za ta sa ido kan yadda ake rubuta labaran fim (wato ‘scripts’).
Bugu da ƙari, shugaban ya gargaɗi masu shirya finafinai da ke zagaye hukumar su na sakin fim ba tare da an ba su izini ba.
Ya ce, “Duk da yake mu na sane da wasu da ke karya doka su na fitar da finafinai ba tare da sun biyo ta hukumar NFVCB ba, mu na so ɗalibai su fahimci ayyukan hukumar saboda su ilmantu da su.”
A cewar sa, gwamnati na so ta ga cewa masu shirya finafinai su na fito da finafinan da su ka dace da tarbiyya da nufin kare ƙananan yaran Nijeriya daga illolin da ke faruwa a cikin al’umma.
Copyright © Fim Magazine. All rights reserved.
www.fimmagazine.com
![]()






