HUKUMAR Gidajen Rediyo da Talbijin ta Nijeriya (Nigerian Broadcasting Corporation, NBC) ta haramta sanya waƙar ‘Warr’ ta Ado Gwanja a dukkan gidajen rediyo da talbijin da ke ƙasar nan.
Ofishin shiyyar Kaduna na hukumar ne ya bayyana hakan a cikin wata takardar sanarwar da ya bayar mai ɗauke da kwanan wata 6 ga Satumba, 2022.
Hukumar ta ce ta lura da cewa waƙar ta karaɗe gidajen rediyo da talbijin a faɗin arewacin ƙasar nan, sannan akwai yiwuwar masu gidajen kafafen yaɗa labarai ma ba su saurare ta da kyau ba domin kuwa ta na ɗauke da wasu kalamai na rashin ɗa’a a cikin ta.

“Waƙar na nuna cewa shan kayan maye karɓaɓɓen al’amarin rayuwa ne,” inji hukumar.
Ta ci gaba da ba da misalan wasu kalmomi da waƙar ta ƙunsa kamar haka:
“…kafin a san mu ai mun ci ƙashin uban mu…”
“…Za ni zo bari in shafa hoda, ko kin zo da ke da hodar ki uban ki zan ci, warr…”
“…Kowa ya ce zai hana mu uban sa zan ci…”
Hukumar ta ce: “Bidiyon waƙar na nuna shan giya kai-tsaye, wanda hakan ya saɓa wa sashe na 3.18.2 (c) da na 3.9 na dokar yaɗa bayanai ta hanyar rediyo da talbijin da ta ce, ‘Gidan rediyo ko talbijin ya tabbatar da cewa wajen watsa bayanai ta kafar sa ya nuna kyakkyawan hali’.”
Mujallar Fim ta riga ta ba da labarin yadda wata kotun shari’ar Musulunci da ke Jihar Kano da kuma Sufeto-Janar na ‘yan sanda su ka ba da umarnin ‘yan sanda su binciki Ado Gwanja kan wannan waƙar da ma ɗayar da ya rera mai suna ‘Chass’.
![]()






