HUKUMAR ‘yan sanda ta Nijeriya (NPF) ta kori wasu jami’an ta uku daga aiki waɗanda su ke tsaron lafiyar mawaƙin siyasa Dauda Adamu Abdullahi Kahutu (Rarara) a bisa laifin rashin iya aiki.
A ranar Juma’a, 7 ga Afrilu, 2023 ne wani bidiyo ya ɓulla a soshiyal midiya inda aka ga ‘yan sandan su na harba bindiga sama a garin Kahutu da ke cikin Ƙaramar Hukumar Ɗanja a Jihar Katsina lokacin da Rarara ya je raba kayan tallafin azumi.
Sun yi haka ne don su tarwatsa cincirindon matasa da su ka taso wa mawaƙin a lokacin da ya ke shirin komawa Kano.
‘Yan sandan, waɗanda su na aiki ne a Sashen Kare Lafiya na Musamman (Special Protection Unit, SPU, Base 1) da ke Kano, su ne Sufeto Ɗahiru Shu’aibu, Saje Abdullahi Badamasi, da Saje Isah Ɗanladi.
A sanarwar da Kakakin NPF, Mista Muyiwa Adejobi, ya fita a jiya Alhamis, wadda mujallar Fim ta samu kwafe, ya ce: “An kori jami’ai uku da ke SPU Base 1 Kano daga aiki saboda laifuffukan ɗabi’ar rashin hankali da rashin iya sarrafa bindiga, nuna ƙarfin ikon da bai dace ba, babban rashin ɗa’a, da ɓarnar lafiyayyen albarushi.”
Ya ce korar tasu ta biyo bayan kukan da aka kai wa hukumar da kuma binciken da ta yi kan al’amarin.
A cewar Adejobi, duk su ukun an gurfanar da su a gaban kotun ‘yan sanda wadda Babban Alƙalin Rundunar ‘Yan Sanda, wato Force Provost Marshal, ya jagoranta.
Abin da su ka aikata, ba su kula da haɗarin da ka iya samun jama’ar da ta taru a wajen ba, ciki har da ƙananan yara, inji shi.
Kakakin ya ce: “Abin da su ka yi ba ma kawai babban laifi ba ne da kuma rashin iya aiki, a’a, abin tozarci ne ma ga Hukumar ‘Yan Sanda da ma ƙasar nan baki ɗaya.”
Ya ce saboda haka NPF na gargaɗin jami’an ta da ko yaushe su riƙa gudanar da aikin su bisa dokokin da aka shimfiɗa don gudun hukunci.
![]()







