TSOHON Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Arewa (AFMAN), Alhaji Hamisu Lamiɗo Iyan-Tama, ya yi kira da a yi adalci ga waɗanda su ka yi tafiyar siyasar Injiniya Abba Kabir Yusuf har ya samu damar lashe zaɓen zama gwamnan Jihar Kano.
Iyan-Tama ya bayyana haka ne a saƙon da ya tura wa mujallar Fim, kwana ɗaya bayan hirar musamman da ta yi da shi kan sakamakon zaɓen.
Iyan-Tama ya ce, “Ita siyasa dace ce; za ka ga wasu sun bauta mata amma ko kaɗan idan an ci zaɓe sai a manta da su. Waɗanda su ka ƙi tafiyar sai su shigo su yi babakere.”
Ya ci-gaba da cewa, “Ina tabbatar maka da cewa yanzu za ka fara ganin wasu daga cikin ‘yan fim ɗin da ba su yi tallar Abba ko kaɗan ba za su fito su ce su nasa ne ko kuma ai sun taimaka, bacin kuma ƙarya su ke yi. Allah ya sa Abba ya san su.”
Babban furodusan kuma shugaban kamfanin Iyan-Tama Multimedia, Kano, ya yi kira ga zaɓaɓɓen gwamnan da ya taimaka wa waɗanda su ka yi masa hidima ta basira da lokaci da shigo da jama’a don su zaɓe shi.
Ya kafa da misali Sunusi Oscar 442, Abba El-Mustapha, Maibulala, Tijjani Gandu, Abubakar Sani da sauran su, ya na faɗin: “Ai ba wanda zai ce bai san su ba a tafiyar Abba.”
Iyan-Tama ya ce: “Ina ba da shawara a yi duba, a yi adalci. Kar a sake a yi abin da ake ce wa kura da shan bugu gardi da kwashe kuɗi.”
Mujallar Fim ta ruwaito cewa yanzu haka tun kafin a je ko’ina har wasu ‘yan fim da su ka yi adawa da Abba Gida-Gida sun fara dawowa su na cewa su da ma can ‘yan Kwankwasiyya ne.
Babban misali shi ne Mustapha Badamasi Naburaska, wanda a baya tafiyar Abba ya yi, amma ya koma tsagin su ɗan takarar jam’iyyar PDP, Dakta Yusuf Gawuna, har Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ba shi muƙamin mataimaki na musamman a ɓangaren farfaganda, amma yanzu ya dawo ɓangaren Abba bayan an lashe zaɓe. Akwai kuma Ali Artwork, Hudu Mazaje da wasun su waɗanda da ɗai-ɗai da ɗai-ɗai za su yi ta dawowa.