JARUMAR Kannywood, Maryam Aliyu Obaje, wadda aka fi sani da suna Madam Korede ko ‘Yar Fim, ta bayyana cewa a taya ta da addu’a domin ta tafi makaranta.
Tun a daren Juma’a ne Madam Korede ta shaida wa mujallar Fim cewa, “In Allah ya kai mu ranar Lahadi, zan tafi makaranta kamar yadda na sanar da ku kwanaki cewa na samu makaranta a Jamhuriyar Benin. Don haka a taya ni da addu’a.”
A yau Lahadi jarumar ta wallafa wani bidiyo a Instagram inda ta ke ɗauke da akwatuna biyu na kayan ta a tashar mota a Kaduna, ta na bin waƙar ‘D’Ja’ ta mawaƙi Yoruba Demon.

A cikin watan Agusta, mujallar Fim ta ruwaito cewa Madam Korede ta samu gurbin karatu a wata jami’a mai suna ‘ESGT Benin University’ da ke Kwatano, babban birnin Jamhuriyar Benin.
Mai makarantar da kan shi ne ya ba ta ‘scholarship’, wato tallafi ko ɗaukar nauyin yin karatun.
Allah ya ba da sa’a, ya sa a fara lafiya, a ƙare lafiya.
![]()







