
JARUMAR Kannywood A’isha Ahmed Idris (Aishatulhumaira) ta kai gudunmawa a gidan yari na Kurmawa da ke birnin Kano.
A ranar Litinin, 20 ga Oktoba ne jarumar ta kai tallafin kayayyakin amfanin yau da kullum a gidan gyaran halin domin taimaka wa fursunoni.
Kayan da ta kai sun haɗa da bokitai 150, kayan ɗanɗanon girki katan 10, garin sabulun wanki katan 10, gidan sauro 50, butar alwala dozin 12, katifu 20, da tabarmi 50.
Da man dai A’isha ta shahara kan ayyukan jinƙai da taimakon al’umma masu ƙaramin ƙarfi da marayu wanda ko a baya ta sha biya wa ɗaurarru masu ƙananan laifuffuka tarar kuɗaɗen da aka saka masu domin su shaƙi iskar ‘yanci.
Ba wannan ne karo na farko da Jaruman Kannywood suke kai gudunmawar kayan amfanin yau da kullum gidajen yari ba.
Ko a baya irin su Mansurah Isah, Hadiza Gabon, da Rahama Sadau sun saba kai makamancin irin wannan tallafin.
Fursunoni da ma’aikatan gidan yarin suna yabawa da jinjina wa A’isha Humaira kan wannan ƙoƙari da take yi.