FITACCIYAR jarumar Kannywood, Hafsat Ahmad Idris, ta yi aure a asirce a jiya Asabar, 26 ga Fabrairu, 2022.
An ɗaura auren a Kano ba tare da an gayyaci ɗan fim ko ɗaya ba, irin yadda wasu ‘yan fim ɗin Hausa su ke yi.
Hakan ya sa ba mu gano wanene ta aura ba da inda aka ɗaura auren da sadakin da aka biya da kuma waliyyan ango da amarya.
Wata majiya ta kurkusa da jarumar, wadda ake wa laƙabi da ‘Ɓarauniya’ saboda fim da ta yi mai wannan sunan, ta shaida wa wakilin mu cewa an tsara cewa babu wata walimar auren da za a yi kuma amarya za ta tare ne ba tare da ɓata lokaci ba.
Mujallar Fim za ta ci gaba da bincike domin gano wasu bayanan game da ɗaurin auren.
Ita dai Hafsat Idris, bazawara ce kuma uwar ‘ya’ya shida – mata huɗu, maza biyu.
Idan kun tuna, a watan Maris na 2021 ta aurar da ɗiyar ta ta uku, wato Khadija Kabir, wadda kuma a kwanan baya ta haihu.
Ta na daga cikin kyawawan jarumai mata waɗanda aka san su da iya shiga da tsadaddun kayan ado.
Mu na mata fatan Allah ya ba su zaman lafiya.
![]()







