Fitaccen jarumi a Kannywood, Ali Dawayya, shi ma dai a yanzu ya raba ƙafa inda baya ga kasancewar sa jarumi kuma furodusa, a yanzu ya buɗe wani sabon gidan sayar da abinci na zamani mai suna Zabuja Restaurant.
A ranar Lahadi 3 ga Nuwamba 2024 ne aka yi taron bikin buɗe gidan abincin na Zabuja Restaurant dake Gidan Dan’asabe a kan titin gidan Zoo a Kano.
Taron buɗe gidan abincin wanda fitaccen Jarumi kuma M D na Hukumar Bunƙasa Fim ta Ƙasa, Ali Nuhu, tare da Ahmad Salisu Alkanawy suka jagoranta, ya samu halartar ‘yan fim da dama inda aka taru domin taya Jarumi Ali Dawayya buɗe sabon gidan sayar da abincin.

Ali Dawayya ya shaida wa mujallar fim manufar sa ta buɗe wajen sayar da abincin, inda yake cewa “A gaskiya na yi farin ciki da ganin jama’a masu yawa da suka halarci wannan taron na buɗe gidan abincin musamman Ali Nuhu da Ahmad Salisu Alkanawy da suka jagoranci buɗewar. Ina yi wa kowa fatan alheri.
“Wannan gidan sayar da abincin da na buɗe, na yi shi ne domin samar wa da kaina mafita, domin a yanzu harkar rayuwa ta wuce a tsaya ga sana’a ɗaya saboda yadda yanayi ya sauya.

“To mu kuma a harkar mu ta fim sai ka ga mun tsaya ga ita kawai duk da ɗimbin buƙatu na rayuwa da suke ƙaruwa, don haka na ga baya ga kasancewa ta a matsayin Jarumi kuma furodusa, to ya zama wajibi na samar da wata hanyar dogaro saboda rayuwa kullum ta na sauyawa ne.
“Kuma a yanzu harkar abinci harka ce ta yau da kullum shi ya sa na zaɓi na buɗe wajen sayar da abincin kuma na samar da duk wani abinci na zamani don buƙatar masu saye, ko su zo su ci a nan ko su tafi da shi, ko kuma a je a kai musu a duk inda suke.
“Ina Godiya ga Allah, kuma ina godiya ga dukkan mutanen da suka halarci wannan taron na buɗe gidan sayar da abincin da na yi mai suna Zabuja Restaurant. Allah ya sa mun buɗe a sa’a.”
![]()







