KWAMITIN shirya Bikin Baje-kolin Finafinai na Harsunan Afrika na Kano, wato Kano Indigenous Languages of Africa Film Market and Festival (KILAF Awards) na bana ya sha alwashin ci gaba da ƙarfafa wa matasan Nijeriya gwiwa wajen samar da finafinai na gargajiya da ke tallata ɗabi’u da al’adun nahiyar ta hanyar fasahar zamani.
Shugaban shirya bikin, Alhaji Abdulkareem Muhammad, shi ne ya bayyana haka yayin taron manema labarai da aka gudanar a ofishin ƙungiyar ’yan jarida ta Nijeriya (NUJ) a Kano a jiya Lahadi don bayyana yunƙurin sa na tunkarar bikin na bana da za a yi shi a watan Nuwamba mai zuwa.
Alhaji Abdulkareem ya ce bikin KILAF ɗin, wanda shi ne karo na takwas, ya karɓi finafinai 616 daga ƙasashe 717, yayin da ƙasashe 12 za su shiga sahun masu karɓar baƙunci.
Ya ƙara da cewa a yayin shirin taron, an buga mujallu guda shida da za su taimaka ga masana harkar finafinai da jami’o’i wajen koyar da sana’ar.
“Akwai ƙasashe 14 da ke fafatawa domin lashe kyaututtuka, wasu daga cikin finafinan ma haɗin gwiwa ne da ƙasashen Birtaniya, Amurka, Isra’ila da Italiya,” inji shi.
Ya ce za a zaɓi masu nasara daga jerin finafinai da aka gabatar ta hannun alƙalai bakwai, kuma za a bayyana sakamakon a ranar 8 ga Nuwamba, 2025.
Ya ci gaba da cewa: “Akwai rukunai 18 na kyaututtuka da za su fito daga cikin nominations 87, kuma kowanne ɗan takara ya cancanci yabo saboda ƙwarewar da ya nuna.
“Don haka KILAF na taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa ilimi da nazari a fannin shirya finafinai, kuma muna alfahari da bayar da gudunmawa a wannan fage.”
Shugaban ya bada sanarwar cewa za a gudanar da taron ƙarfafa wa mata 100 masu shiga harkar kafafen yaɗa labarai gwiwa a karo na biyu a wani sabon ɓangare da aka ƙara a bara wanda zai gudana a Makarantar Kasuwanci ta Ɗangote (Dangote Business School) da ke Jami’ar Bayero, Kano, a ranar 8 ga Nuwamba daga ƙarfe 10 na safe zuwa 2 na rana.
A cewar sa, an tsara shirin ne domin ƙarfafa shiga da nasarar mata a harkar kasuwancin kafafen yaɗa labarai.
Ya ce: “Za mu gayyato mahalarta daga kafafen yaɗa labarai, ƙungiyar mata ’yan jarida (NAWOJ), ƙungiyar mata (NCWS), da ƙarfafa ƙungiyoyin kare haƙƙin mata.
“KILAF tana fatan ganin sabbin haziƙan matasa da mata suna amfani da finafinai wajen kare martabar harshen gida da al’adun Afrika.”
![]()







