BABBAR Kotun Jihar Kano da ke Bompai, Kano, a jiya ta haramta wa fitacciyar jarumar TikTok Murja Ibrahim Kunya yin amfani da soshiyal midiya.
Haka kuma kotun, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Nasiru Saminu, ta bayar da beli ga Murja kan kuɗi N500,000.
Wasu tsauraran sharuɗɗan belin sun haɗa da cewa ta kawo mutum biyu da za su tsaya mata, waɗanda dole ɗaya daga cikin su ya kasance ɗan’uwan ta na kusa yayin da ɗayan zai kasance ya mallaki ƙasa mai daraja a Jihar Kano.
Kotun ta kuma hana Murja sanya duk wani saƙo ko yin martani a kafafen sada zumunta na zamani kamar su TikTok, Facebook, Instagram da sauran su har na tsawon lokacin da za ta kasance ƙarƙashin zaman belin.
Kotun ta umarci Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar da ya riƙa bibiyar halin da jarumar ta ke ciki don ganin ba ta saɓa wa haramcin yin amfani da kafafen sada zumuntar ba.
Kotun ta halasta wa kwamishinan da ya kama jarumar tare da gaggauta miƙa ta ga kotu muddin ya same ta da ƙeta haramcin amfani da zaurukan na sada zumunta.
Kotun ta kuma bayar da umarni ga Hukumar Asibitoci ta Jihar Kano da Asibitin Kula da Ƙwaƙwalwa na Gwamnatin Tarayya da ke Dawanau su kawo wa kotun rahoton gwajin ƙwaƙwalwar Murja a cikin kwana bakwai.
Tun a makonnin da su ka gabata dai Murja ta shigar da ƙara a gaban kotun, ta na ƙalubalantar Babban Mai Shari’a na jihar.
A ƙarar da ta shigar, ta nemi a yi mata tsakani da su.
Murja ta haɗa da Alƙalin Kotun Shari’ar Musulunci, Alhaji Nura Yusuf Ahmad, da Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano da Hukumar Hisbah ta Jihar Kano da Hukumar Asibitocin Jihar Kano da Asibitin Kula da Masu lalurar ƙwaƙwalwa na ƙasa da ke Dawanau.
Takardar ƙarar tun a wancan lokacin ta nuna cewa Babbar Kotun ta cimma muradu huɗu daga cikin jerin buƙatu bakwai da lauyoyin Murja su ka gabatar wa Mai Shari’a Nasiru Saminu.
Sai dai daga cikin buƙatun da kotun ta yi watsi da su har da ta neman mayar mata da wayar ta ta hannu ƙirar iPhone da kuma katin ATM na banki.
Haka kuma ta nemi kotun da ta sanya Asibitin Muhammad Abdullahi Wase da Asibitin Kula da Ƙwaƙwalwa na Gwamnatin Tarayya da ke Dawanau su ba lauyoyin ta rahoton gwajin ƙwaƙwalwar ta.
Bayan karanta sharuɗɗan belin sai alƙalin ya ɗage sauraren shari’ar zuwa ranar 16 ga Mayu, 2024.
Ana iya tuna cewa a bayan nan dai Mai Shari’a Malam Nura Yusuf Ahmad na Kotun Shari’ar Musulunci da ke Kwana Huɗu, Kano, ya bayar da umarnin a yi wa Murja gwajin ƙwaƙwalwa.
Mai Shari’a Nura Yusuf ya ba da umarnin yi wa Murja gwajin ne a asibitin gwamnati domin tabbatar da ƙoshin lafiyar ta.
Alƙalin ya ba da umarnin ne bisa zargin jarumar ba ta cikin hayyacin ta a lokacin zaman kotun na farko da aka gurfanar da ita.
Tun da farko dai Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ce ta yi ƙarar jarumar kan zargin tayar da hankalin jama’a, ɓata tarbiyya da kuma koyar da karuwanci.
![]()







