WATA kotu a Kano da ke yin shari’a bisa tuhumar jarumar TikTok Murja Ibrahim Kunya da wasu mutum uku da aikata baɗala a jiya ta ba da umarnin a mayar da su gidan yari inda ake tsare da su.
Mutum ukun su ne Ashir Idris (Maiwushirya), Aminu BBC da mawaƙi Sadiq Shehu Shariff.
Idan kun tuna, a ranar 16 ga Fabrairu, 2023 mujallar Fim ta ruwaito labarin yadda ‘yan sanda sun kama mutanen tare da gurfanar da su a gaban kotun a bisa tuhumar su da kalaman batsa da ɓata tarbiyya. Amma sun musanta zargin.
Tun da fari, wata ƙungiya mai suna Zauren Malaman Kano ce ta kai kukan matasan ga ‘yan sanda.
A zaman da aka yi jiya Alhamis, 23 ga Fabrairu, an kara karanto wa su Ashir Maiwushirya da sauran biyun da ake tuhuma laifin su kamar yadda lauyan su, Barista Mustapha Alimi, ya buƙata.
Lauyan ya nemi kotun da ta ba da dama a ƙara karanto masu laifin su domin su na buƙatar su sauya musantawa zuwa amsa laifi, kuma nan take kotu ta bayar da damar. Bayan an karanto masu ɗin sai kuma nan take su ka amsa laifin.
Ita kuwa Murja, lauyoyin ta sun sanar wa kotu da cewa sun samu daidaito da lauyoyi masu gabatar da ƙara, inda kuma kotun ta tambayi lauya mai gabatar da ƙara, Barista Lamiɗo Soron Ɗinki ko sun yi hakan? Sai ya amsa da cewa haka ne, kuma ya buƙaci kotun da ta ba shi damar ya koma ofishin lauyan Murja domin ya karɓo takardar saboda a zaman da su ka yi ba a sanya wa takardar hannu ba.
Kotu ta amince da roƙon nasa.
Shi kuma lauyan Murja, Barista A.D. Saka, ya nemi kotu da ta ba da belin wadda ake ƙara.
Alƙali ya ce ai da man tun a baya an yi magana kan roƙon beli.
A nan ne aka samu wata cacar baki tsakanin lauyan Murja da na gwamnati, har ta kai ga an tafi hutu.
Ana shirin dawowa ne kuma sai aka samu labarin cewa garin ya na cikin wani yanayi na rashin tsaro saboda artabun siyasa tsakanin ‘yan Kwankwasiyya da ‘yan Gandujiyya, don haka sai aka ɗage zaman shari’ar zuwa ranar 2 ga Maris.
Kotu ta sake aikawa da su Murja gidan yari har zuwa ranar da za a koma domin ci gaba da shari’ar.