• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, August 12, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Mawaƙin hip-hop Nomiis Gee ya bayyana matsayin sa kan siyasa

by DAGA ABBA MUHAMMAD
September 18, 2022
in Labarai
0
Aminu Nomiis Gee da Dakta Gawuna

Aminu Nomiis Gee da Dakta Gawuna

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

FITACCEN mawaƙin gambara (hip-pop) kuma mai gabatar da shirin nan mai farin jini na ‘Zafafa 10’ da a tashar Arewa 24, Aminu Abba Umar (Nomiis Gee), ya bayyana matsayin sa a kan harkokin siyasa da ake cikin yi a yanzu, ya ce shi siyasar sa ta aƙida ce ba ta kuɗi ba.

Mawaƙin ya faɗi haka ne lokacin da ya ke yi wa mujallar Fim bayani kan dalilin ziyarar da aka gan shi ya kai wa ɗan takarar zama gwamnan Kano a jami’iyyar APC kuma kuma Mataimakin Gwamnan jihar a yanzu, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, kwanan nan.

A hoton shi da Gawuna da ya wallafa a Instagram, mai gabatar da shirin ya bayyana ɗan siyasar da “next Kano State Governor 2023 Insha Allah”, wato “Gwamnan Kano da zai hau a 2023 in Allah ya yarda”, wanda hakan na nuna inda bakin sa ya karkata a yanzu.

A tattaunawar da ya yi da wakilin mu, Nomiss Gee ya bayyana wasu alaƙoƙi da ke tsakanin sa da wasu manyan ‘yan siyasar Kano.

Ya ce: “Kakakin majalisar Jihar Kano, dangin mu ne shi. Shi kan shi Sha’aban Sharaɗa tare mu ka yi karatu da shi. A.A. Zaura kuwa ajin mu ɗaya da shi. Ni ne dai kawai ba na so in yi nan in yi can.

“Amma kuma shi Gawuna tun tuni na ke tare da shi, ba yanzu ba, tun mu na jami’a. In faɗa maka, tun ya na ciyaman na ƙaramar hukuma, kafin ya zama kwamishina. 

Daga dama: Mataimakin Gwamna, Dakta Gawuna, tare da Aminu Abba Umar (Nomiis Gee) a lokacin ziyarar

“Sannan ƙanen sa kuma aboki na ne. Wani lokaci mu kan zauna ‘on a personal level’, mu yi maganar mu. A lokacin da mu ka gama makaranta shekara takwas zuwa goma da su ka gabata, shi ya ɗauki nauyin dukkan abin da mu ka yi da sauran ɗalibai da abokai na.”

Mawaƙin ya ce waɗannan alaƙoƙin sun sanya shi ya kasa gane wanne zai goya wa baya a siyasar.

Ya ce: “Abin ya zama na rasa ina ma zan yi; duk inda na juya sai in ga akwai nawa, hankali duk ya rabu. Kuma da ma can ni ANPP na ke yi, tun a wancan lokacin. Amma ka san yanzu Arewa 24 ka na aiki da kamfani ba za ka iya fitowa ka ce za ka riƙa yin wasu abubuwa ba. Ka san babu ruwan su da maganar siyasa, sai a wannan karon kamar mutum ya na da damar yin talla ko ‘jingle’ ya karɓa, duk da wasu ba iya biyan kuɗin su ke yi ba. Amma kuma ni na yanke a zuciya ta wanda na daɗe ina tare da shi ina mutunci da shi, kuma ‘fan’ ɗi na ne sosai.”

Nomiis Gee ya ci gaba da cewa, “A ranar ma ina kan hanya zan dawo daga Nijar ya kira ni ya ce mani ya na ke, kwana biyu? Na ce masa gani nan zuwa gidan, sai ya ce ai da ma ya na jira na. Kuma ko da na je ba maganar siyasa mu ka yi ba. Hira kawai mu ka yi, ya na tambaya na ina su wane da wane. Kawai daga baya ne ma na ce to wai menene, tunda ina tare da shi bari ma kawai na goya masa baya.  

“Amma ina da siyasar da na ke yi. Nan ba da jimawa ba mutane za su gani. Amma ba wai kawai zan zo ina bin wani ba, ko in je can a ba ni wata dubu ɗaya ko wani abu, wannan ba shi ba ne. Ni ina yin abin da zai taimaki al’umma ne. 

“Kuma Gawuna mutumin kirki ne, ba shi da matsala, ga shi da hankali, ba za ka taɓa jin shi da wata matsala ba. Kuma shi babu ruwan shi da ka na yin sa ko ba ka yin sa, in ya tashi taimakon ka, taimakon zai yi.

“Wannan hoto da aka gan ni tare da shi ake tambaya abin da ya kai ni wurin sa, ba komai ba ne illa ziyarar sada zumunci.”

Nomiis Gee ya faɗa wa mujallar Fim yadda ‘yan takara daban-daban su ke ta zawarcin sa saboda alaƙar sa da matasan Nijeriya. Ya ce: “Maganar siyasa, ko a satin nan akwai mutanen PDP ‘yan Atiku su na ta kira na, wallahi ba na ɗaukar wayar su! Kai, jam’iyyu da dama su na kira na tun tuni, kowa na so ya kira ni saboda matasa, an san mu ke da matasa, amma ba na son irin wannan siyasar da za ka shiga cikin ruɗu. In ina yin mutum kawai ina yin sa. 

“Akwai waɗanda su ka kira ni su ka ce in ba da suna na za su sai mani tikitin jirgi in je Abuja in same su. Ina ganin kamar mutanen Manjo Hamza Al-Mustapha ne. Sai na faɗa masu gaskiya ina ‘busy’!”

Loading

Tags: A.A. ZauraAminu Abba UmarArewa 24Atiku AbubakarDakta Nasiru GawunaNomiis GeeSha'aban Sharaɗa.siyasaZaɓen 2023Zafafa 10ziyara
Previous Post

Dawayya ta shawarci mata masu tallar jikin su a TikTok

Next Post

Na daɗe a Kannywood, yanzu na fara hango haske a harkar – Hauwa Tamburawa

Related Posts

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama
Labarai

Fitaccen mawaƙin siyasa Muhammadu Buhari ‘Kosan Waka’ ya kwanta dama

August 2, 2026
Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11
Labarai

Yadda gwajin ƙwayoyin halitta na jini ya kawo ƙarshen auren Adam A. Zango da Maimuna Musa bayan watanni 11

August 1, 2026
Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano
Labarai

Jami’an gwamnati sun yi zama da Kannywood domin fara aiwatar da shirin ba da inshorar lafiya kyauta ga ‘yan fim na Kano

July 15, 2026
Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu
Labarai

Kannywood tana buƙatar farfaɗo da gidajen sinima domin bunƙasa tattalin arzikin ƙirƙira – Sani Mu’azu

July 14, 2026
A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti
Labarai

A hira da mujallar Fim, mawaƙi Ado Gwanja ya aiko da saƙo ga masoyan sa daga gadon asibiti

July 9, 2026
Next Post
Hauwa Mukhtar Tamburawa

Na daɗe a Kannywood, yanzu na fara hango haske a harkar - Hauwa Tamburawa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!