• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 13, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

MOPPAN da AFMAN kaɗai mu ka yarda su yi wa ‘yan fim sabuwar rajista, inji El-Mustapha

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
August 22, 2023
in Labarai
0
Alhaji Abba El-Mustapha

Alhaji Abba El-Mustapha

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

SHUGABAN Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Alhaji Abba El-Mustapha, ya bayyana cewa Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN) da Kungiyar Masu Shirya Finafinai ta Arewa (AFMAN) su ne gwamnati ta yarda da su su yi wa kowane ɗan fim ɗin Hausa rajista.

 Ya faɗi haka ne a lokacin da ya ke yi wa mujallar Fim ƙarin bayani kan yadda hukumar sa za ta yi wa ‘yan Kannywood rajista.

Idan kun tuna, jim kaɗan bayan ya ɗare kujerar shugabancin hukumar ya ba da sanarwar cewa hukumar za ta ba da lasisin ga duk wani mai sana’a a cikin kannywood, amma daga baya ya damka alhakin sabunta lasisin a hannun ƙungiyoyin ‘yan fim.

Tun daga lokacin jama’a su ke tambayar lokacin da za a fara yin rajistar da tsarin za a bi wajen sabuntawar.

A hirar sa da wakilin mu a ofishin sa kan al’amarin, El-Mustapha ya ce, “Wannan dama ce ta ƙungiyoyi da tun a baya su ka rasa, wadda a yanzu mu ka mayar musu da ita, saboda ‘yan fim su su ka san kan su a ƙungiyance, don haka zai fi sauƙi idan su su ka tantance kan su.”

Sai dai ya ce duk da haka damar da aka ba ƙungiyoyin, hukumar ba za ta zuba masu ido ba.

“Za mu samar da wakilai masu saka ido don ganin aikin ya tafi daidai, don haka akwai wakilai daga Hukumar Tace Finafinai, Hukumar Hisbah, Hukumar Shari’a da za su yi aiki tare don ganin abin ya tafi daidai,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa, “Akwai ƙungiyoyi na ‘yan fim da yawa, amma dai a yanzu mun zaɓi ƙungiyar MOPPAN da ta Arewa domin gudanar da aikin wanda a ƙarƙashin su ne duk wani ɗan fim zai yi rajista ya zama halastaccen ɗan fim da hukuma a Jihar Kano za ta yarda da shi.

Kuma abin da na ke so mutane su sani, mun zaɓi waɗannan ƙungiyoyin guda biyu ne domin samun daidaito, domin da wuya ka samu wani ɗan fim a Kano da ba ya cikin waɗannan ƙungiyoyin.

“Ni kai na ai ka ga akwai ƙungiyar mu ta AHPIP kuma ta na nan har yanzu, akwai ƙungiyoyin mata ‘yan fim; duk ban saka su ba saboda ba na so abin ya yi yawa don kada ya haifar da rashin tsari. Don a yanzu so mu ke mu ga an haɗe kan ‘yan fim don su zama tsintsiya-maɗaurin-ki-ɗaya.

“Kuma ka gane, ni ɗan fim ne da na ke a matsayin jarumi, darakta, furodusa, don haka duk wani abu da ake gudanarwa a cikin harkar na sani. Duk wanda zai zo mana da wasa ba za mu saurara masa ba. Za mu yi abin mu ne cikin tsari domin samun nasarar da mu ke buƙata.”

Loading

Previous Post

Kannywood: Abin da ya sa na tafi na dawo – Alhassan Kwalle

Next Post

Don in cike gurbin adabi ne zan fitar da littafin waƙoƙi na mai suna ‘Dausayin Fasaha’ – Gidan Dabino

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON

Don in cike gurbin adabi ne zan fitar da littafin waƙoƙi na mai suna 'Dausayin Fasaha' - Gidan Dabino

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!