• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, July 2, 2025
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

by ABBA MUHAMMAD
June 29, 2025
in Labarai
0
MOPPAN ta yi wa al’ummar Kano ta’aziyyar Aminu Ɗantata 

Marigayi Alhaji Aminu Ɗantata

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

ƘUNGIYAR Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN) ta miƙa saƙon ta’aziyyar rasuwar hamshaƙin ɗan kasuwa Alhaji Aminu Ɗantata ga Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, da al’ummar jihar.

Ƙungiyar ta yi saƙon ne ta wasiƙa wadda shugaban ta na riƙo, Alhaji Shehu Hassan Kano, ya rattaba wa sannu.

Ƙungiyar ta ce, “Cikin tsananin baƙin ciki da tsananin rashi muka samu labarin rasuwar hamshaƙin ɗan kasuwa kuma fitaccen ɗan Kano, Alhaji Aminu Ɗantata.

“Alhaji Ɗantata ba wai kawai wani babban jigo ne a harkar kasuwanci a Jihar Kano da Afrika ta Yamma ba, har ma ya kasance mai kishin al’umma, mai taimakon jama’a, kuma abin koyi.

“Jagorancin sa na hangen nesa, basirar kasuwanci, da zuba jari a ɓangarori daban-daban sun taimaka wajen bunƙasa tattalin arziki, samar da damarmaki marasa adadi da kuma ɗaukaka al’umma da suka wuce iyakokin Kano.

“Gudunmawar da ya bayar a fannin kasuwanci da masana’antu sun bar tarihi a cigaban yankin.

“Rasuwar sa babban rashi ne ba ga dangin sa da ’yan kasuwa kaɗai ba, har ma ga ɗaukacin Jihar Kano da ma yammacin Afirka.

“Abubuwan da ya gada na sana’a, karamci da jajircewar sa na cigaba za a tuna da su kuma za a girmama su har wasu lokuta masu zuwa.”

Ƙungiyar ta cigaba da cewa, “A cikin wannan lokaci mai cike da alhini, muna miƙa ta’aziyyar mu ga mai girma gwamna, da gwamnatin Jihar Kano da ɗaukacin iyalan Ɗantata, ‘yan kasuwa, da ɗaukacin al’ummar Kano baki ɗaya.”

Allah Ta’ala ya gafarta masa kurakuran sa, ya saka masa da Jannatul Firdaus, ya kuma bai wa iyalan sa, abokan sa da al’ummar Kano haƙurin jure wannan babban rashi da ba za a iya maye gurbin sa ba.

Alhaji Aminu Ɗantata dai ya rasu ne a Abu Dhabi da ke ƙasar Haɗaɗɗun Daulolin Larabawa (UAE) a jiya Asabar, kuma ana sa ran za a binne shi a Madina kamar yadda ya yi wasici. Shekarun sa 94 a duniya.

Loading

Tags: Abu DhabiAminu ƊantataMadinaMOPPANrasuwata'aziyya
Previous Post

Jaruman Kannywood, Abdul M. Shareef da Maryam Malika sun zama ɗaya

Next Post

Al-Ameen, Haidar na shirin Daɗin Kowa, ya zama angon Walida

Related Posts

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta
Labarai

Ƙungiyoyin harkar fim, KAFIGAN da MOPPAN, sun yi wa Rahama Sadau ta’aziyyar rasuwar mahaifin ta

June 23, 2025
Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau mutumin kirki ne da son jama’a, inji Yerima Shettima

June 22, 2025
Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau
Labarai

Yadda mahaifin mu ya rasu kwana ɗaya bayan ya dawo daga Makkah – Abba, yayan Rahama Sadau

June 22, 2025
Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji
Labarai

Mahaifin Rahama Sadau ya rasu kwana 1 bayan ya dawo daga aikin Hajji

June 22, 2025
Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano
Labarai

Masanin harshe, Korao Hamadou ya gabatar da haruffan rubutun Hausa na asali a taro a Kano

June 20, 2025
Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza
Labarai

Kotu a Kano ta tsare Tsulange, matashin da ke tare titi yana wanka da yin shigar banza

June 20, 2025
Next Post
Al-Ameen, Haidar na shirin Daɗin Kowa, ya zama angon Walida

Al-Ameen, Haidar na shirin Daɗin Kowa, ya zama angon Walida

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!