A JIYA Asabar, 29 ga Disamba, 2023, jarumin Kannywood Isma’il Ishaq Koli, ya angwance
An ɗaura auren Isma’il da abar ƙaunar sa, Nasira Zakariyya Aliyu, a Masallacin Juma’a na Government College Kaduna da misalin ƙarfe 1:00 na rana bayan an yi sallar Juma’a, a kan sadaki N100,000.
An yi walima a harabar masallacin bayan an ɗaura aure.
Haka kuma, an yi wata walimar a gidan su ango da ke Kakuri Road, unguwar Rafin Guza, a Kaduna.

Wakilin mujallar Fim da ya halarci ɗaurin auren ya ruwaito cewa ‘yan fim da su ka halarci ɗaurin auren sun haɗa da Yakubu Lere, Rabi’u Koli, Salisu Salinga, Abubakar Hunter, Nura MC Khan, Yaroskhan Abubakar, Ishaq Ɗantsoho da Hamisu Bawasa.
Haka kuma abokan aikin angon, wato ‘yan jarida, su ma sun halarta daga gidajen rediyo da talbijin da su ka haɗa da JKD TV, FRCN, Karama FM, Liberty FM, Liberty TV, Vision FM, Nagarta Radio, KSMC TV, Kada FM, DITV, Alheri Radio da Invicter FM.



![]()






