ALLAH ya yi wa fitacciyar jarumar Kannywood, Wasila Isma’il, rasuwa a yau Lahadi, lamarin da ya girgiza ba ma masana’antar finafinan Hausa kaɗai ba har ma da sauran al’umma.
Wasila ta rasu a yammacin yau a Asibitin FOMWAN da ke unguwar Badarawa, a garin Kaduna, sakamakon ciwon suga da ta daɗe tana fama da shi, sai kuma bugun zuciya da aka ce shi ne ajalin ta.
Shekarun ta kimanin 46 a duniya.
Wasila ta rasu ta bar ‘ya’ya huɗu, mata uku da namiji ɗaya, waɗanda suka haifa tare da tsohon mijin ta, wato jarumi kuma darakta Al-Amin Ciroma.
‘Ya’ya biyar suka haifa, amma namiji ɗaya ya rasu tun tuni.
Ita da Ciroma, wanda fitaccen ɗan jarida ne, sun rabu shekaru uku da suka gabata bayan sun shafe kusan shekaru 21 suna zaman aure.
Ƙasa da shekara ɗaya kafin mutuwar auren, wato a ranar Alhamis, 6 ga Oktoba, 2022 Ciroma da Wasila suka yi bikin cikar su shekara 20 da aure.
Rabuwar auren, wadda mujallar Fim ce ta fara ba da labarin shi a ranar 4 ga Yuli, 2023, ta girgiza masu karatu.
Masoyan jaruman biyu sun yi ƙoƙarin sasanta su domin su koma auren, amma abin ya ci tura.
Daga bisani Wasila ta sake dawowa harkar fim, inda ta cigaba da ƙoƙari wajen bayar da gudunmawa a fannoni daban-daban na masana’antar ta Kannywood tare da nuna jajircewa wajen tallafa wa cigaban masana’antar.
Wata majiya ta ce mutane da dama da suka gan ta a jiya ba su kawo mata mutuwa kusa ba domin an gan ta tana harkokin ta cikin ƙoshin lafiya, har ma ta ziyarci mutane a gidajen su.
Rasuwar tata ta girgiza masana’antar Kannywood matuƙa. ‘Yan fim da sauran jama’a suna ta bayyana alhinin su tare da yi mata addu’a, musamman a soshiyal midiya.
Ciroma ya wallafa alhinin sa a shafin sa na Facebook, inda ya ce: “Innaa lillahi wa innaa ilaihi raaji’uuun. Allah Ta’ala Ya yi wa Malama Wasila Ismail Rasuwa.
Allah Ya gafarta ma ta, mu ma Allah Ta’ala Ya sa mu gama lafiya Ameeeen.”
Saƙon ya ja hankalin jama’a matuƙa, inda aka dinga yi wa marigayiyar addu’ar samun rahama.
An faɗa wa mujallar Fim cewa ba za a yi jana’izar marigayiyar a yau ba saboda yamma ta yi sannan ga garin da hadari.
Sai gobe za a yi jana’izar da ƙarfe 10:00 na safe a gidan su da ke Shagari Junction da ke Badarawa, kusa da tsohon ofishin ubangidan Wasila, wato Yakubu Lere.
Allah ya jiƙan Wasila, ya gafarta mata kurakuran ta, ya sanya Aljannar Firdausi ta zama makoma a gare ta, sannan ya kyautata rayuwar ‘ya’yan ta, amin.
![]()







