ALLAHU ya yi wa matashin jarumin barkwanci a Kannywood, Kamal S. Aboki, rasuwa a yau.
Kamal wanda ɗan asalin Maiduguri ne kuma mazaunin Kano, ya rasu sanadiyyar haɗarin mota da ya ritsa da shi a kan hanyar sa ta zuwa Kano daga Maiduguri.
Rasuwar Kamal ta ɗaga hankalin ‘yan fim, domin duk inda ka leƙa a soshiyal midiya hotunan sa ne da bidiyoyin sa ke yawo a jimamin rashin sa, musamman ganin shi yaro ne matashi.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa Kamal ya fara wasan barkwanci ne a Instagram, inda ya ke yin gajerun bidiyoyi ya na ɗorawa a shafukan sa, daga nan kuma ya koma YouTube.
Marigayin ya na da masoya da mabiya da dama, kasancewar wasannin da ya ke yi su na nishaɗantar da jama’a.
Jarumi Abdullahi Amdaz, wanda ya na da kusanci da marigayin, ya bayyana jimami kan rasuwar Kamal, ya na cewa: “Kamal ɗaya ne daga cikin mutanen da su ka ɗauke ni tamkar ciki ɗaya mu ke. Ya na karɓar shawarat’ ta, ya kan kira ni ya gai da ni, ya zo inda na ke. Babban abin da yake burge ni da shi girmama mutane da fara’a.

“Ba zan manta wannan ranar ba. Kamal Aboki ya ce da ni , ‘Oga bari na yi maka hoto, zan ajiye tarihin na yi tafiya da kai zuwa Maiduguri!’ Mu na wasa da dariya, na ce, ‘Ka ji ka da zolaya sai ka ce ka yi tafiya da wannan babban mutum!'”
Da ya tuno da wannan abu, sai Amdaz ya ce: “Cikin hukuncin Allah, ashe hoton ne zai zama tarihin ka a guri na. Allah ya yi maka rahama Kamal, domin Kamal ba ɗan barkwanci ba ne kawai, mutum ne mai hankali l, natsuwa da girmama mutane.
“Allah ya sani, ban san wani aibun Kamal da zan iya faɗa a duniya ba. Wannan ta sa dole mun ji zafin mutuwar sa, amma duk son da mu ke yi masa Allah ya na masa wanda ya fi namu, shi ya sa ya kira shi zuwa gare shi.
“Allah ya gafarta masa yasa aljanna makomar sa.”
To, amin ya Allah.

![]()








Comment:Allah yagafartamasa yasa aljanna makoma intamu tazo Allah yasa mucika da imani Amen