SHUGABAN Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi ta’aziyya ga iyalai, abokan aiki da masoyan fitacciyar jarumar Kannywood, Hajiya Saratu Giɗaɗo, wadda ta rasu a ranar Talata a Kano.
Mai ba shugaban ƙasar shawara kan aikin jarida da yaɗa labarai, Cif Ajuri Ngelale, ya faɗa a cikin takarda ga manema labarai cewa Shugaba Tinubu ya bayyana rasuwar ‘yar fim ɗin ‘yar shekara 56 a matsayin abin baƙin ciki, “ba kawai ga waɗanda aka yi wa rasuwar ba har ma ga ƙasar baki ɗaya, wadda ta yi wa aiki ta hanyar basirar ta a matsayin ta na ‘yar wasa.”
A cikin takardar, wadda mujallar Fim ta samu kwafen ta, shugaban ya ce ban da giɓin da rasuwar ta ta bari a masana’antar nishaɗantarwa da ke ƙara haɓaka, za kuma a yi matuƙar kewar ayyukan taimakon jama’a da Saratu Giɗaɗo ta riƙa yi.
Shugaban Ƙasar ya aika da saƙon ta’aziyya ga gwamnatin Jihar Kano da dukkan waɗanda rasuwar
Hajiya Saratu Giɗaɗo ta shafa, sannan ya yi addu’ar Allah ya jiƙan ta.
![]()







