• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 13, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Ya yi ƙarar jarumar Kannywood Hadiza Gabon a kan zargin ta ci masa kuɗi ta ƙi auren sa

by DAGA MUHAMMAD LAWAN RANO
June 6, 2022
in Labarai
0
Hadiza Aliyu Gabon

Hadiza Aliyu Gabon

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

WANI mutum mai suna Bala Musa ya maka fitacciyar jarumar Kannywood Hadiza Gabon a kotun shari’ar Musulunci a Kaduna bisa zargin ta yaudare shi ta ci masa kuɗi a kan za ta aure shi. 

Mutumin, ɗan shekara 48, ya maka jarumar a kotun ne bisa laifin yaudarar ma’aikacin gwamnati.

Mujallar Fim ta ruwaito cewa an fara zaman sauraron ƙarar ne tun a ranar 23 ga Mayu, 2022 amma ita Hadizar ba ta je kotun ba.

A zaman da aka yi a yau Litinin, 6 ga Yuni, 2022, mai ƙarar ya bayyana wa kotu cewa sun kwashe tsawon lokaci su na soyayya da jarumar, har ta kai ga sun yi alƙawarin yin aure a tsakanin su kuma ta aminta da haka.

Bala Musa ya ƙara da cewa, ”Haka jarumar ta yi ta sa ni ina yi mata hidima a duk lokacin da ta ke da buƙata ba tare da tunanin abin da zai je ya dawo ba, domin kuwa na gama yarda da za mu yi aure, wanda  zuwa yanzu na kashe wa jarumar zunzurutun kuɗi kimanin naira 396,000.”

A cewar sa, ”Haka kuma jarumar ta kauce wa haɗuwar mu a garin Gusau da ke Jihar Zamfara, inda a nan na ke da zama, bayan na gama dukkan wani shiri da ya kamata.”

To sai dai a nata ɓangaren, Hadiza Gabon ta musanta zargin, ta ce tun da fari ba ta ma tabbatar da sahihaccin sammacin da aka kai mata ba, shi ya sa ba ta bayyana a gaban kotun ba. 

Lauyan ta, Mubarak Kabiru, wanda ya wakilce ta, ya ce, ”Duba da irin shaharar wadda na ke karewa, ta na haɗuwa da mutane daban-daban masu wata manufa ta daban. Ita mace ce mai tsantseni da kula domin samun kariya da tsaro.”

Lauyan ya roƙi kotun da ta ba shi lokaci domin ya gabatar da wadda ake ƙara a gaban kotun. 

Mai Shari’a Malam Rilwanu Kyaudai ya ɗage ci gaba da sauraron ƙarar zuwa ranar 13 ga Yuni, 2022.

Loading

Tags: aureBala MusaHadiza GabonjarumaKadunaKannywoodkotuƙaraRilwanu KyaudaiShari'ar Musuluncituhuma
Previous Post

Auren mawaƙi Lilin Baba da jarumar Kannywood Ummi Rahab: Sauran kwana 14

Next Post

Cewar minista Sadiya ga ɗaliban shirin ‘N-Build’ 40,000 da aka yaye: Horaswar da ku ka samu za ta taimaki rayuwar ku a ko’ina

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Minista, Hajiya Sadiya Umar Farouq, na miƙa satifiket da kayan aiki ga wata naƙasasshiya da aka ba horaswar yin sana'a

Cewar minista Sadiya ga ɗaliban shirin 'N-Build' 40,000 da aka yaye: Horaswar da ku ka samu za ta taimaki rayuwar ku a ko'ina

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!