KWAMITIN Zaɓe na Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN) ya fitar da tsarin yadda za a gudanar da babban taro da kuma zaɓen ƙungiyar a Lafiya, babban birnin Jihar Nassarawa, a ranar Asabar, 18 ga Janairu, 2025.
A cikin sanarwar musamman da ya fitar a yau, Sakataren kwamitin, Malam Ibrahim Ibrahim, ya ce ana sa ran dukkan wakilai masu kaɗa ƙuri’a, wato dalaget, da kuma ‘yan takara su isa garin a ranar Juma’a, 17 ga Janairu.
Ya ce za a tantance ‘yan takarar a dai wannan ranar ta Juma’a.
Sakataren ya ƙara da cewa washegari da safe, wato Asabar, za a yi babban taro tare da jin manufofin ‘yan takara da kuma zaɓe.
A tsarin, za a rantsar da sababbin shugabannin ƙungiyar da yamma a wannan rana ta Asabar, wato da ƙarfe 4.
Za a yi bankwana da juna tare da watsewa a ranar Lahadi, 19 ga wata.
Ibrahim ya ba da lambobin waya da mai buƙatar ƙarin bayani zai iya kira ya yi tambaya, wato 08038690968 da 07069108030.
Sakataren ya ce: “Muna fatan a yi wannan muhimmin taro cikin nasara tare da kira ga dukkan dalaget da ‘yan takara da su fito baki ɗaya a yi komai tare da su.”
Mujallar Fim ta ruwaito cewa an yi ta ƙila-wa-ƙala a kan yiwuwar yin taron a Jihar Nassarawa saboda ba a samu tabbacin ko gwamnatin jihar za ta ɗauki nauyin sa ba kamar yadda MOPPAN ta buƙata.
Sai a yau ne takarda ta fito daga ofishin Gwamna Abdullahi Sule inda ya ba da amincewar ɗaukar nauyin babban taron na MOPPAN a Lafiya.
Sakamakon haka ne kwamitin zaɓen ya fitar da tsarin yadda za a gudanar da taron da zaɓen, wanda haka ya saka farin ciki a zukatan ‘ya’yan ƙungiyar.
![]()







