• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Wednesday, May 6, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Zaɓen MOPPAN ta Sokoto: Bello Achida da Baban Umma na so a yi zaɓe cikin nasara

by DAGA ABBA MUHAMMAD
December 9, 2022
in Labarai
0
Daga hagu: Malam Bello Achida da Malam Sharif Usman Baban Umma

Daga hagu: Malam Bello Achida da Malam Sharif Usman Baban Umma

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

MAI Binciken Kuɗi na 2 (Auditor 2) na Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa (MOPPAN), Malam Bello Achida, ya yi kira ga ‘yan takara da su yi aiki tare idan aka kammala zaɓen ƙungiyar reshen Jihar Sokoto da za a yi a ranar Lahadi mai zuwa, 11 ga Disamba, 2022.

Uwar ƙungiyar ta ƙasa ce ta naɗa Achida domin ya wakilce ta a wurin zaɓen don tabbatar da an yi zaɓen a cikin nasara.

A tattaunawar sa da mujallar Fim, Alhaji Bello ya ce, “Ina godiya ga Allah da ya nuna mana wannan lokaci da za a gudanar da wannan zaɓe. ‘Tenure’ na shugabannin MOPPAN na Jihar Sokoto ta ƙare tun a watan Agusta na shekarar 2021, ana ta kai ruwa rana, ana ta fitintunu, amma yanzu an kai ƙarshe, har na ba da dama na a je a yi zaɓe, kuma har an kai an sa rana. 

“Duk abubuwan da su ka gudana tsawon shekara ɗaya da aka yi, ni uwar ƙungiya ta wakilta, har aka yi nasara.”

Achida ya ƙara da cewa, “Ina roƙo, idan aka yi zaɓe, waɗanda su ka yi nasara su riƙe waɗanda ba su yi nasara ba a yi tafiya tare, su kuma waɗanda Allah bai ba nasara ba, sai su yi haƙuri nasu lokacin ya na nan tafe. Ina fatan a yi wannan taron lafiya, a ƙare lafiya.”

A sanarwar da shugaban kwamitin zaɓen, Sharif Usman Baban Umma ya fitar, ya ce, “A madadin kwamitin zaɓen MOPPAN na Jihar Sokoto, mu na sanar da duk wani mamba wanda ke da rajista da cewa za a gudanar da zaɓen sababbin shugabanni da kuma tantance mambobi haɗi da rantsar da sababbin shugabanni. Amma za a fara tantance mambobi da misalin ƙarfe 9:00 na safe, da fatan za a zo a kan lokaci.”

Za a gudanar da zaɓen a ɗakin taro da ke sakatariyar Ƙaramar Hukumar Sokoto ta Kudu, da misalin ƙarfe 11:00 na safe.

Allah ya ba da ikon zuwa, ya kuma sa a yi lafiya.

Loading

Tags: Bello AchidafurodusoshiMOPPANSharif Usman Baban Ummasokotozaɓe
Previous Post

Abubakar Sani ya yi sababbin waƙoƙi, kuma ya faɗi dalilin rashin jin ɗuriyar sa

Next Post

Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya ta karrama mawallafin Blueprint, Mohammed Malagi

Related Posts

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim
Labarai

Rasuwar dattijon Kannywood, Nura Shareef, ta girgiza ‘yan fim

February 22, 2026
Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza
Labarai

Daraktar fim ta ƙi karɓar awad saboda kisan gillar da Isra’ila take yi a Gaza

February 21, 2026
Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai
Labarai

Fitaccen furodusa Kunle Afolayan ya yi haɗin gwiwa da Jamhuriyar Benin kan shirya finafinai

February 19, 2026
An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa
Labarai

An naɗa Farfesa Tengya matsayin sabon shugaban Cibiyar Koyon Finafinai ta Ƙasa

February 15, 2026
Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6
Labarai

Alƙali ya ci Samha Inuwa tara ko ta je kurkuku wata 6

February 13, 2026
Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira
Labarai

Hukumar EFCC ta kama jarumar Kannywood, Samha Inuwa, saboda goge majina da takardun naira

February 3, 2026
Next Post
Ana karrama mawallafin Blueprint da Manhaja, Alhaji Mohammed Idris Malagi (na 4 daga dama)

Ƙungiyar 'Yan Jarida ta Nijeriya ta karrama mawallafin Blueprint, Mohammed Malagi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!