• Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
Tuesday, August 25, 2026
  • Login
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai da Rahotanni
    • Labarai
    • Rahotonni
    • Tattaunawa
  • Sharhi da Tsokaci
    • Sharhin Fim
    • Tsokaci
  • Masu Haskawa
    • Taurarin Fim
    • Marubuta
    • Mawaƙa
  • Addini da Rayuwa
    • Rayuwa
    • Iyalai
    • Al’adu
    • Addini
  • Ranar Murna
No Result
View All Result
Kannywood - News, reviews and more  › hausa
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

Za mu samar da cibiyar koyar da sana’ar fim a Kano – Gwamna Ganduje

by DAGA MUKHTAR YAKUBU
October 4, 2022
in Labarai
1
Gwamnan Kano, Dakta Ganduje, a wajen taron

Gwamnan Kano, Dakta Ganduje, a wajen taron

0
SHARES
0
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsappShare on Telegram

A ƘOƘARIN da ta ke yi na samar da bunƙasar masana’antar finafinai ta Kannywood, gwamnatin Jihar Kano ta sha alwashin samar da wata cibiya domin koyar da harkar fim.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ne ya sanar da hakan a lokacin da ya ke buɗe taron sanin makamar aiki wanda gwamnatin jihar ta ɗauki nauyin gudanarwa a otal ɗin Central da ke Titin Bompai a ranar Lahadi.

Gwamnan ya ce, “Duba da irin muhimmancin da sana’ar fim ta ke da shi a duniya mu ka ga ya kamata mu samar maku da wasu hanyoyi na inganta sana’ar ku yadda za ta tafi da zamani da kuma ilimi. Don haka ne mu ka samar da wani tsari a yanzu na koyar da ku dabarun sanin makamar aiki da kuma ilimi a cikin harkar taku, shi ya sa mu ka taru a wannan waje domin buɗe fara koyar da ku da za a yi na tsawon kwanaki biyar saboda ku ƙara sanin yadda harkokin kasuwancin naku ya ke.”

Gwamnan ya ce hakan ya samu ne a sakamakon yadda gwamnatin sa ta damu da sana’ar fim kamar yadda su ma ‘yan fim ɗin su ke ba gwamnati goyon baya wajen gudanar da al’amurran ta.

Ya ƙara da cewa, “Duba da irin alaƙar ku da wannan gwamnati ya sa mu ka zaɓi wasu daga cikin ku mu ka saka su a cikin ƙunshin gwamnatin mu domin ku ma ku ba da taku gudunmawar a matsayin ku da ku ka daɗe ku na bayar da goyon baya a tafiyar da gwamnati.

Wassu mahalarta yaron

“Ga Afakallahu nan, ɗan cikin ku ne mu ka ba shi Hukumar Tace Finafinai ya ke riƙe da ita. Kuma ga Mustapha Badamasi Nabraska shi ma S.A. ne na Farfaganda, da kuma wani babba a cikin ku da mu ka ba shi babban mai ba da shawara a kan Kannywood. Don haka mu na tare da ku kamar yadda ku ke ba mu goyon bayan ku.”

Gwamnan ya ce, “Bayan wannan hosarwa da za a yi maku, mu na da burin gina maku sabuwar cibiyar koyar da dabarun harkar fim a wannan jiha. Amma aikin zai yiwu ne idan kun haɗa kan ku kun samar da tsari a tsakanin ku, wanda hakan ne zai sa a samar da ƙwararru da za su tafiyar da harkar cibiyar.

“Don haka ina kira a gare ku da ku haɗa kan ku domin tafiya tare. Mu kuma a namu ɓangaren na gwamnati, za mu samar muku tsare-tsare masu muhimmanci a kan masana’antar ku.”

Tun da farko da ya ke nasa jawabi, shugaban Gidauniyar Kannywood, Malam Shu’aibu Yawale, ya bayyana Dakta Ganduje a matsayin gwamnan da ya bai wa masana’antar Kannywood kulawar da babu wani gwamna da ya taɓa ba ta.

Ya ce: “Babu shakka, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje shi ne gwamnan da ba a taɓa samun wani gwamna da ya ke kula da masana’antar Kannywood kamar sa ba, domin an ɗauki mutane daga cikin mu an saka su a cikin harkar gwamnati, an ɗauki nauyin karatun wasu daga cikin mu, za su tafi ƙasashen waje karatu. A yanzu kuma mu na taro ne na buɗe koyar da mu ilimin harkar fim aƙalla mutane 450 

“Don haka a kullum mu ke godiya tare da jinjina ga wannan gwamnati. Kuma a shiye mu ke mu bayar da duk wata gudunmawar da ta dace don ganin gwamnati ta cimma manufofin ta da ta sa a gaba.”

Shi kuwa a nasa jawabin, malami a Jami’ar Bayero kuma masani kan harkar fim, Farfesa Abdalla Uba Adamu, kira ya yi ga ‘yan fim da su gane cewa shi fim ba kasuwanci ba ne, sana’a ne, don haka su daina tunanin samun kuɗi a lokaci guda.

Ya ce: “Duk ƙasashen da su ka ci gaba a harkar fim sun ɗauki harkar fim ne a matsayin sana’a, don haka su ke samun cigaba. Amma mu namu finafinan mun tsaya har yanzu a kan rawa da waƙa. Tun da aka faro harkar daga bidiyo aka koma sidi zuwa dibidi, har yanzu abu ɗaya ne. Babu wani abu da ake nunawa na zahirin al’adun Bahaushe ko ilimin sa da sana’o’in sa.

“Saboda haka, a yanzu da duniya ta canza aka koma YouTube, ya kamata a samu wani sauyi da za a riƙa kallon rayuwar Hausawa da cigaban da su ke da shi.”

Hadiza Mohammed, Asma’u Sani da su Teema Makamashi a taron

Mujallar Fim ta ruwaito cewa taron ya samu halartar jama’a masu yawa daga cikin masana’antar Kannywood, kuma an yi waƙoƙin siyasa tare da tallata jam’iyyar APC a wajen, wanda hakan ya sa wasu ke ƙorafin ko dai Dattawan Kannywood sun sayar da masana’antar da gwamnati ne.

An kammala taron da shirya liyafar cin abincin dare a Gidan Gwamnati, inda aka zaɓi wasu daga cikin ‘yan masana’antar aka kai su su ka ci abinci tare da gwamna.

Gwamna Ganduje, Farfesa Abdalla da sauran manyan baƙi a ƙarshen taron

Loading

Tags: Abdalla Uba AdamuAbdullahi Umar GandujeAPCcibiyahoraswaliyafaMustapha NabraskaShu'aibu Yawale.Zaɓen 2023
Previous Post

Rahama Sadau ta yarfa wa Mansurah raddi kan batun takarar Tinubu

Next Post

Rikicin mawaƙa: Ummi B.Y. ta maka El-Mu’az Birniwa a kotu a Kaduna

Related Posts

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe
Labarai

Mutuwar aure na ƙaddara ce – Jaruma Khadija Yobe

August 23, 2026
Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi
Labarai

Aina’u Ade ta raba wa tsofaffin jaruman Kannywood tallafin kuɗi

August 23, 2026
Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti
Labarai

Ƙungiyar ‘Triple R Kannywood’ ta ziyarci jarumi Tanimu Akawu a asibiti

August 23, 2026
Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000
Labarai

Ƙungiyar Triple R ta ba jarumin Kannywood Mustapha Musty tallafin N500,000

August 18, 2026
Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye
Labarai

Yadda na gamu da ibtila’in karaya a ƙafa – Jarumi Ɗan’azumi Kamaye

August 14, 2026
Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba
Labarai

Tozali TV zai yi bikin Henna Ball da karrama masu ƙwazo da tallafa wa waɗanda suka tsira daga hare-hare a ranar 31 ga Oktoba

August 8, 2026
Next Post
Ummi B.Y. da El-Mu'az Birniwa

Rikicin mawaƙa: Ummi B.Y. ta maka El-Mu'az Birniwa a kotu a Kaduna

Comments 1

  1. Pingback: Za mu samar da cibiyar koyar da sana’ar fim a Kano – Gwamna Ganduje - LastNg

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

  • Home
  • Game Da Mu
  • Privacy Policy
  • Contact Us

© 2024 Mujallar Fim

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labari
  • Addini
  • Al’adu
  • Iyali
  • Marubuta
  • Mawaƙa
  • Nijeriya
  • Ranar Murna
  • Rayuwa
  • Sharhin Fim
  • Tattaunawa
  • Taurari
  • Tsokaci

© 2024 Mujallar Fim

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!