GWAMNATIN Tarayya ta bayyana cewa za ta taka wa kamfonin da ke yaɗa finafinai da waƙoƙi a intanet ko talbijin burki domin za a iya amfanin da su a jawo fitina a Nijeriya.
Ministan Yaɗa Labarai da Kyautata Al’adu, Alhaji Lai Mohammed, shi ne ya bayyana haka a wajen babban taron da Hukumar Tace Finafinai ta Ƙasa (NFVCB) ta yi da irin waɗannan kamfanonin shekaranjiya a Legas.
Idan kun tuna, mujallar Fim ta ba ku labari a ranar 28 ga Nuwamba, 2021 cewa ana kiran shirye-shiryen da waɗannan kamfanonin ke yaɗawa ta hanyar intanet ko talbijin da‘OTT’ (wato ‘over-the-top content’).
Sun haɗa da finafinai, waƙoƙi ko shirye-shiryen talbijin, kuma kamfanonin na tura wa mai buƙata ta hanyar intanet ko akwatin talbijin a bisa irin buƙatar sa, kuma zai riƙa biyan kuɗi.
Kamfanonin da ke yaɗa su a Nijeriya sun haɗa da Netflix, Amazon, Showmax, Africa Magic, YouTube, Northflix, Iroko TV da ire-iren su.
A jawabin da ya gabatar a wajen buɗe taron na kwana biyu ne minista Lai ya faɗi matsayin gwamnati a kan shirye-shiryen, inda ya yi nuni da cewa kamfanonin da ke yaɗa su sun ƙara samun farin jini da karɓuwa ga jama’ar Nijeriya tun daga lokacin zaman dole da annobar korona (COVID-19) ta jawo, “shi ya sa za a ɗora su a bisa turbar doka.”

Ministan, wanda Daraktar Yaɗa Labarai da Kimiyya a ma’aikatar sa, Madam Comfort Ajiboye, ta wakilta, ya yi nuni da cewa za a iya amfani da kamfanonin “a jawo fitina” kuma a yi wa tsarin dimokiraɗiyyar Nijeriya zagon ƙasa.
Tun da fari sai da Babban Darakta kuma Shugaban Hukumar Tace Finafinai ta Ƙasa, Alhaji Adedayo Thomas, ya gabatar da jawabin buɗe taron, inda ya bayyana cewa an kira taron ne domin a yi musayar ra’ayi kan yadda za a fito da sababbin manufofi da tsare-tsare a gwamnatance waɗanda za su yi aiki a kan masu yaɗa shirye-shirye ta hanyar yanar gizo ko talbijin a Nijeriya.
Ya ce, “Da yake waɗannan shirye-shirye su na isa ga sama da kashi 50 cikin ɗari na al’ummar mu, ya zama wajibi mu kira wannan taron inda za a tattaro masu ruwa da tsaki da masu tsara dokoki domin su tattauna saboda a fito da bayyanannun tsare-tsare kan ɗora masu yaɗa shirye-shirye a intanet da talbijin da kuma masu ƙirƙirar shirye-shiryen bisa turbar doka.”
Shugaban ya ce kamfanonin yaɗa shirye-shiryen sun kasa kimtsa kan su da kan su domin bin doka, wanda hakan ne ya jawo har ake tattaunawa a kan su a yau.
Thomas ya sha alwashin cewa, “Ba burin fito da wannan doka ba ne ya takure fasaha, amma dai ana so ne a daidaita sahu tare da inganta gasa mai tsafta don cigaban al’umma da tattalin arziki.”
A taron, jami’an gwamnati da na kamfanonin yaɗa shirye-shirye a intanet da talbijin da sauran masu ruwa da tsari a al’amarin, irin su ‘yan fim, sun tattauna kan jigon taron, wato “Al’amuran Dokokin Tace Finafinai na Nijeriya da Tsarin Kawo Gyara Ga Kamfanonin Yaɗa Finafinai da Bidiyo da Masu Ƙirƙirar Shirye-shiryen Kallo,” wato a Turance, “Implications of Nigerian Censorship Laws and Regulatory Framework for OTT Streaming Services and Content Providers”.
Daraktan Kula da Tsare-tsaren Jama’a na kamfanin Netflix mai kula da yammacin Afrika, Shola Sanni, na ɗaya daga cikin mahalarta taron.

Mujallar Fim ta fahimci cewa tsohon shugaban Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), wadda ita ce uwar ƙungiyoyin masu harkar finafinan Hausa, Dakta Ahmad Sarari, kusam shi kaɗai sanannen ɗan fim da ya halarci taron daga Kannywood.
Akwai kuma membobin ƙungiyoyi daban-daban na masana’antar shirya finafinai ta Nollywood waɗanda su ka haɗa da ƙungiyar jarumai (AGN) da ta daraktocin fim (DGN) da na mamallaka gidajen sinima da sauran su sun halarci taron.
Haka kuma akwai wakilan kamfanonin yaɗa shirye-shirye a intanet na cikin gida da na ƙasashen waje, da na gidajen talbijin masu amfani da satalayit, da kuma masu ƙirƙirar shirye-shirye waɗanda da Turanci ake kira ‘content creators’.
An yi taron a otal ɗin ‘Radisson Hotel’ da ke unguwar Ikeja GRA a Legas a ranakun 1 da 2 ga Disamba, 2021.



Ai yan kannywood babu kishin masana’antar a ran su, domin mafi yawan su neman kudi ne yasa suke cikin ta. Shiyasa za ayi ta tarurruka amma ace mutum daya ne a cikin su zai halarta, wani sa’in ma babu ko mutum guda, kaico!!