SABON Shugaban Ƙungiyar Ɗaliban Harshen Hausa ta Jami’ar Bayero, Kano, Malam Kabiru Yusuf Fagge (Anka), ya sha alwashin zai kawo sauye-sauye da za su canza yadda ake tafiyar da ƙungiyar a baya.
Ya faɗi haka ne bayan an zaɓe shi a matsayin sabon ƙungiyar a ranar Juma’a a zangon karatu na 2022/2023.
Anka, wanda ɗalibi ne a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya inda yake karatun digirin farko a fannin harshen Hausa, fitaccen marubucin littattafan Hausa da finafinan Kannywood ne.
An zaɓe shi tare da wasu masu dafa masa su 11 da suka haɗa da Nasiru Abubakar a matsayin Mataimakin Shugaba; Hisnuddin Auwal Tahir, Magatakarda; Umar Nasir, Mataimakin Magatakarda; Isa Garba Usman, Jami’in Shirye-shirye, da Khadija Yahaya Ɗanjuma, Jami’ar Walwala.
Akwai kuma Zulaihat Safiyanu da aka zaɓa a Ma’aji; Zubairu Ɗahiru Turaki, Jami’in Hulɗa Da Jama’a na farko (PRO 1); Mujahid Mansur; Mataimakin Jami’in Hulɗa Da Jama’a (PRO II); Jami’ar Wayar Da Kai Da Wasanni; Amina Sunusi Shamaki; da Hajara Shu’aibu Muhammad, Jami’ar Kuɗi.

Kabiru Yusuf Fagge ya ce ya karɓi wannan shugabanci ne domin kawo sauye-sauye da yake ganin za su canza yadda ake tafiyar da ƙungiyar a baya.
Daga cikin abubuwan da yake da burin ganin ya samar domin farfaɗo da Ƙungiyar Hausa ta BUK akwai shirya tarukan wayar da kai ga sababbin ɗalibai, shirya tarukan sanin makamar karatu a zangon karatu da uwa-uba shirya taron Ranar Hausa da ake yi a ƙungiyar.
Haka nan kuma ya na so ya ga an gyara ofishin ƙungiyar da samar da littattafai don ɗalibai, da samar da motar zirga-zirga ta ƙungiya.
Sannan idan suka kammala wannan zango na shugabancin za su shirya zaɓe don a fitar da wasu shugabannin.
Mujallar Fim ta ruwaito cewa shi dai wannan zaɓe ana gudanar da shi ne a duk bayan shekara a kowane zangon karatu domin samar da sababbin shugabanni, musamman saboda ‘yan aji 4 za su tafi sai a maye gurbin su.
Ana yin zaɓen ta hanyar kafa Hukumar Zaɓe, tare da bai wa ɗalibai damar yin zaɓe a junan su, ƙarƙashin kulawar hukumar makarantar.
Kuma ana zaɓo sababin shugabannin ne daga ‘yan aji na 1 zuwa na 4, sai dai an fi zaɓar ‘yan aji na 4 a matsayin shugaba da mataimaki ko sakatare.
An dai kafa Ƙungiyar Hausa ta BUK ne kamar sauran ƙungiyoyin jami’o’i domin haɓaka wannan sashe na Hausa aiwatar da tarukan da suka shafi cigaban harshen Hausa da al’adun Hausawa. Kuma ƙungiyar ta ce za su riƙa sanin darajar ilimin da su ke koya da kuma fito da kyawawan ayyukan sashen na Hausa.
![]()







