ALLAH ya albarkaci furodusa a Kannywood, Abdulrahaman Gambo (Ɗangwal), da ‘ya mace.
Matar sa A’isha Muhammad ta haihu da misalin ƙarfe 8:02 na dare a gidan sa da ke lamba A 321, Sabon Titin Kwaɗo, kwanar Masallacin Dillalai, Katsina, a ranar Litinin, 1 ga Mayu, 2023.
Ɗangwal ya raɗa wa jaririyar suna A’isha, ya na kiran ta da ‘Yargwal.
Za a yi bikin suna a ranar Litinin mai zuwa.

An dai ɗaura auren Ɗangwal da A’isha ne a ranar Asabar, 4 ga Yuni, 2023, a masallacin Juma’a na Sheikh Abubakar Mahmud Gumi da ke Titin Sabon Birni, Sabon Kawo, Kaduna.
Ɗangwal furodusa ne ɗan asalin Jihar Katsina, amma ya na gudanar da harkokin sa na finafinai a Kaduna.
Ɗangwal ya taɓa fitowa takarar zama ɗan majalisar jiha mai wakiltar Funtuwa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP na shekarar 2023, sai kuma bai samu damar cin zaɓen fitar da gwani ba a 2022.